• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Tuesday, June 23, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Maryam ‘Yar Aljanna (2)

ADABI

Nasir G. Ahmad by Nasir G. Ahmad
June 22, 2026
in Adabi
0
Maryam ‘Yar Aljanna (2)

Labarin Maryam

3
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Maryam ‘Yar Aljanna (2)
__________
Gabatarwa:
Wannan shi ne kashi na biyu kuma na ƙarshe na wannan ƙirƙirarren labari, wanda muka samu daga haziƙin adibi, Malam Nasiru G. Ahmad. Labari ne mai mai cike da abin tausayi da kuma darussa masu yawa. Ga ci gaba daga inda muka tsaya:
__________

Maryam ‘Yar Aljanna

Aka yi sa’a, kuɗin da ake bin mutumin nan daidai suke da abin da ke hannunta, na ladan aikin da ta yi wa malamin nan mai ibada. Nan take ta fitar da kuɗin ta ba su, ta ‘yanta mutumin.

Related posts

Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa

Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa

June 21, 2026
Maryam ‘Yar Aljanna

Maryam ‘Yar Aljanna

June 20, 2026

Mutumin da ta ‘yanta ya tambaye ta wace ce ita? Da ta habarta masa labarinta, sai ya ce in za ta amince zai kasance tare da ita, su nemi arziƙi tare. Ya ce duk abin da suka samu sai su riƙa rabawa tsakaninsu. Ya kuma ce kamata ya yi su hau jirgin ruwa su bar garin.

Matar ta amince, suka nufi bakin kogi.Yayin da suka isa bakin kogi, sai wannan mutum ya ce ta fara shiga jirgin ta zauna. Ya ce mata yana dawowa yanzu. Sai ya je ya sami masu jirgin ya ce musu ga wata baiwarsa can yana son sayar da ita. Suka yi ciniki ya karɓi awalajar, ya arce ya bar ta nan.

Har jirgi ya tashi ba ta ga abokin tafiyarta ba. Masu jirgi suka zo suna duba ta, har suna tattaɓa ta. Da ta yi magana sai suka ce ai sun riga sun saye ta daga wajen ubangidanta, don haka ta ba da kai kawai bori ya hau. Ita kuwa ta ce sam ba ta san wannan zance ba. Suna cikin wannan taƙaddama ne wata guguwa ta tashi cikin kogin, igiyar ruwa ta murɗa, nan take jirgin ya kife. Duk ilahirin mutanen da ke cikin jirgin suka nutse cikin kogi, in ban da wannan baiwar Allah da ta yi sa’ar kama wani allon jirgi, ya yi ta iyo da ita bisa ruwa.

A daidai wannan lokaci sarkin garin ya fito shan iska bakin kogi. Ya kuma ga tasowar guguwar ba a lokutan da ta saba tashi ba. Can sai ya hangi wannan mata tana ta walagigi bisa ruwa. Nan da nan ya ba da umarni, wasu fadawa suka je aka fito da ita. Ya sa aka tafi da ita gidansa. Ya umarci likitansa da ya kula da ita.

Yayin da ta farfaɗo, sarki ya tambaye ta labarinta. Ta zayyana masa duk abin da ya faru gare ta, tun daga ƙazafin ɗan uwan mijinta gare ta, har zuwa azzalumin da ya sayar da ita a matsayin baiwa.

Sarkin ya yaba da halinta da kuma kaifin basirarta. Ya nemi ya aure ta, ta kuwa amince. Saboda kaifin hankalinta, duk abin da sarkin nan zai yi sai ya nemi shawararta.

Labarinta ya yi tambari a duk sassan ƙasar da sarkin ke mulki. Ana nan kan haka, har cutar ajali ta kama sarki, ya faɗi ya mutu. Manyan ƙasa suka zauna shawarar wanda za su naɗa sarki, ra’ayinsu ya haɗu kan ba wanda ya fi cancanta kamar matar sarkin nan. Ba tare da ɓata lokaci ba kuwa suka naɗa ta sarauniyar wannan ƙasa.

Wata rana sarauniya ta yi wani zama a ƙofar fada. Ta nemi a taro mata duk mazajen da ke ƙasar, a bijirar da su gabanta. Nan da nan kuwa kowa ya hallara. Mazaje suka shiga wucewa tana ganin su ɗaya bayan ɗaya. Can sai ga tsohon mijinta wanda ya sake ta ya kuma kore ta. Sai ta sa a tsayar da shi can gefe guda. Ƙanensa da ya yi mata sharri ma ya zo wucewa, ta sa aka tsayar da shi can kusa da ɗan uwansa. Mai ibadar da ta yi wa aiki da hadiminsa da ya kashe ɗan mai ibadar ma haka. Can kuma sai ga azzalumin da ya sayar da ita, shi ma ta sa aka tsayar da shi. Aka ware su can gefe guda.

Bayan an gama bijirar da mazajen, sai ta sa aka kawo waɗancan mutane da ta sa aka tsayar da su zuwa gabanta. Babu wanda ya gane ta daga cikinsu. Ta bayyana musu ko ita wace ce, sannan ta ce da tsohon mijinta: “Haƙiƙa kai ba ka da laifi, ɗan uwanka ne ya ha’ince ka.” Ta sa aka sallame shi. Ta dubi ɗan uwansa ta ce: “Kai kuma za a yi maka bulala tamanin, domin ƙazafin da ka yi wa matar ɗan uwanka.”

Ta sa aka sallami Malam mai ibada tare da yi masa sha tara ta arziƙi. Hadiminsa kuwa ta sa aka fille kansa, domin ya yi kisan kai ga ɗan mai ibadar nan. Shi kuma mutumin da ta ‘yanta amma ita ya sayar da ita, ta sa a ɗaure shi a kurkuku saboda cin amana da ya yi.

Allah shi ne Musawwiru! Tabbas, duk wanda ya dogara ga Allah, zai isar masa sharrin duk wani mai sharri!
__________

Previous Post

Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa

Next Post

Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

Related Posts

Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa
Adabi

Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa

June 21, 2026
Maryam ‘Yar Aljanna
Adabi

Maryam ‘Yar Aljanna

June 20, 2026
Sharhin Littafin Tarihin Rayuwar Sule Lamido
Adabi

Sharhin Littafin Tarihin Rayuwar Sule Lamido

June 8, 2026
Next Post
Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al'ummar Musulmin Arewa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Sanadiyyar Rubutu, Zane Da Waƙa: Na Samu Arzikin Sanin Jama’a – Kamal

Sanadiyyar Rubutu, Zane Da Waƙa: Na Samu Arzikin Sanin Jama’a – Kamal

July 15, 2023
TAURARON GIZAGO: Idris Ibrahim Kubau

TAURARON GIZAGO: Idris Ibrahim Kubau

August 13, 2023
ZUWA GA ‘YAN UWA MUSULMI ‘YAN SHI’A: SHIN DA GASKE KUNA KOYI DA ALI (RTA) NE?

ZUWA GA ‘YAN UWA MUSULMI ‘YAN SHI’A: SHIN DA GASKE KUNA KOYI DA ALI (RTA) NE?

July 23, 2025

October 1, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo
  • Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa
  • Maryam ‘Yar Aljanna (2)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

June 23, 2026
Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

June 22, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.