EMMANUE JOSEPH: YA ZAGI MANZON ALLAH (SAW)

__________
Akwai takaici, akwai baƙin ciki, yadda wannan matashi, mai suna Emmanuel Joseph ya ƙunduma wa Manzon Allah (saw) zagi. Ba zagi irin na kara-zube ba, a’a, sai da ya kama sunansa mai daraja, sannan ya cusa masa irin ta Maguzawa.
Munin zagin ya yi girma ta kowane fanni, dalili ke nan ya sanya ba zan iya ambata shi ba, kuma ba zan iya nuna screenshot a nan ba.
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un! Wai yanzu irin zamanin da muka shigo ke nan! A ce Manzon Allah (saw), wanda ya fi kowa daraja, ya fi kowa tausayi da jin ƙai, wai shi ne abin tozartawa ga wannan al’umma, wacce Allah ya aiko shi MANZO a matsayin rahama a gare mu?
Na san za ku tambaye ni, ta yaya haka ta faru, da har Emmanuel ya saki ruɓaɓɓen bakinsa, ya guma wannan aika-aika?
Na samu wannan abin takaici ne, a yayin da nake sauraren wani malamin Musulunci a TikTok, yana bayanin yadda shi wannan matashi ya ɗauki Alƙur’ani mai girma yana nunawa, yana ɓatanci a kansa. Shi ne malamin ya yi kira ga Hukuma da Jami’an Tsaro na Jihar Kaduna, cewa su ɗauki matakin hukunci a kansa, ko kuma al’ummar Musulmi su hukunta shi da kansu.
Ai kuwa ina bibiyar Comment Section, sai na ci karo da shi dai Emmanuel, ya biyo har zuwa shafin malamin, ya kama sunan Manzon Allah (saw), ya ƙunduma masa irin ta Maguzawa (Hasbunallahu wani’imal wakil)!
To, kai kuwa Emmanuel, me ya kai ka ɗaukar Alkur’ani ka la’ance shi kuma me ya sanya ka zaɓi ka ci mutuncin Manzon Allah (saw)? Lallai na tabbata kai ba Kirista ba ne na ƙwarai, domin babu wani mai bin Annabi Isa (alaihis salam) da gaskiya da zai zagi Manzon Allah (saw).
A nan nake kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna, da ta yi gaugawar bincika wannan al’amari kuma ta hukunta wannan mutum, domin ya zama izina ga masu gigin aikata irin wannan mummunan aiki.
Haka kuma, ina kira ga al’ummar Musulmi da cewa, lallai mu kiyayi yadda muke tafiyar da addininmu. Mu kiyayi zage-zagen ƙungiyoyi da malamanmu, saboda saɓanin fahimta. Na tabbata mutane irin Emmnuel sun samu ƙwarin gwiwar tozarta addininmu ne, ganin yadda mu ma muke tozarta malaman juna, muna zage-zagen ƙungiyoyin juna. Lallai mu sani, sai mun kare addininmu da malamanmu, sannan wasu za su kare su.
Muna roƙon Allah ya yi riƙo da hannunmu, ya ɗora mu kan hanyarsa madaidaiciya, Amin-summa-amin!
_______________
Jama’a, yaya kuke ganin wannan al’amari? Mu ba juna shawara yadda za mu kauce wa cin zarafin addininmu a Comment Section:













wslm idan harda gaske yayi wannan batanci to shine kawai akasheshi annabifa? (saww) ammaduk abinda kefaruwa shine wasu sukabada kofar hakan domin mutum yadogarada wata fahimta kai kuma kanazaginsa kokace ya kauce WA.ATASIMU BIHABLILLAHI JAMI.AN WALATAFARRAQU BILLAHI fadar allahce