• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, March 5, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

EMMANUE JOSEPH: YA ZAGI MANZON ALLAH (SAW)

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
September 12, 2025
in Gizago
1
EMMANUE JOSEPH: YA ZAGI MANZON ALLAH (SAW)

Emmanuel Joseph, wanda ya zagi Manzon Allah (saw)

57
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

EMMANUE JOSEPH: YA ZAGI MANZON ALLAH (SAW)

Emmanuel Joseph, wanda ya zagi Manzon Allah (saw)

__________

Related posts

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)

March 1, 2026
#AdalciGaWalida (01): ƘIRA GA GWAMNATIN JIHAR JIGAWA DA TA ƊAUKI MATAKIN GAUGAWA A KAN KUƁUTAR DA WALIDA ABDULHADI

#AdalciGaWalida (01): ƘIRA GA GWAMNATIN JIHAR JIGAWA DA TA ƊAUKI MATAKIN GAUGAWA A KAN KUƁUTAR DA WALIDA ABDULHADI

February 23, 2026

Akwai takaici, akwai baƙin ciki, yadda wannan matashi, mai suna Emmanuel Joseph ya ƙunduma wa Manzon Allah (saw) zagi. Ba zagi irin na kara-zube ba, a’a, sai da ya kama sunansa mai daraja, sannan ya cusa masa irin ta Maguzawa.

Munin zagin ya yi girma ta kowane fanni, dalili ke nan ya sanya ba zan iya ambata shi ba, kuma ba zan iya nuna screenshot a nan ba.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un! Wai yanzu irin zamanin da muka shigo ke nan! A ce Manzon Allah (saw), wanda ya fi kowa daraja, ya fi kowa tausayi da jin ƙai, wai shi ne abin tozartawa ga wannan al’umma, wacce Allah ya aiko shi MANZO a matsayin rahama a gare mu?

Na san za ku tambaye ni, ta yaya haka ta faru, da har Emmanuel ya saki ruɓaɓɓen bakinsa, ya guma wannan aika-aika?

Na samu wannan abin takaici ne, a yayin da nake sauraren wani malamin Musulunci a TikTok, yana bayanin yadda shi wannan matashi ya ɗauki Alƙur’ani mai girma yana nunawa, yana ɓatanci a kansa. Shi ne malamin ya yi kira ga Hukuma da Jami’an Tsaro na Jihar Kaduna, cewa su ɗauki matakin hukunci a kansa, ko kuma al’ummar Musulmi su hukunta shi da kansu.

Ai kuwa ina bibiyar Comment Section, sai na ci karo da shi dai Emmanuel, ya biyo har zuwa shafin malamin, ya kama sunan Manzon Allah (saw), ya ƙunduma masa irin ta Maguzawa (Hasbunallahu wani’imal wakil)!

To, kai kuwa Emmanuel, me ya kai ka ɗaukar Alkur’ani ka la’ance shi kuma me ya sanya ka zaɓi ka ci mutuncin Manzon Allah (saw)? Lallai na tabbata kai ba Kirista ba ne na ƙwarai, domin babu wani mai bin Annabi Isa (alaihis salam) da gaskiya da zai zagi Manzon Allah (saw).

A nan nake kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna, da ta yi gaugawar bincika wannan al’amari kuma ta hukunta wannan mutum, domin ya zama izina ga masu gigin aikata irin wannan mummunan aiki.

Haka kuma, ina kira ga al’ummar Musulmi da cewa, lallai mu kiyayi yadda muke tafiyar da addininmu. Mu kiyayi zage-zagen ƙungiyoyi da malamanmu, saboda saɓanin fahimta. Na tabbata mutane irin Emmnuel sun samu ƙwarin gwiwar tozarta addininmu ne, ganin yadda mu ma muke tozarta malaman juna, muna zage-zagen ƙungiyoyin juna. Lallai mu sani, sai mun kare addininmu da malamanmu, sannan wasu za su kare su.

Muna roƙon Allah ya yi riƙo da hannunmu, ya ɗora mu kan hanyarsa madaidaiciya, Amin-summa-amin!

_______________
Jama’a, yaya kuke ganin wannan al’amari? Mu ba juna shawara yadda za mu kauce wa cin zarafin addininmu a Comment Section:

Previous Post

SASSANYAN AMINCI (4)

Next Post

SASSANYAN AMINCI (5)

Related Posts

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)
Gizago

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)

March 1, 2026
#AdalciGaWalida (01): ƘIRA GA GWAMNATIN JIHAR JIGAWA DA TA ƊAUKI MATAKIN GAUGAWA A KAN KUƁUTAR DA WALIDA ABDULHADI
Gizago

#AdalciGaWalida (01): ƘIRA GA GWAMNATIN JIHAR JIGAWA DA TA ƊAUKI MATAKIN GAUGAWA A KAN KUƁUTAR DA WALIDA ABDULHADI

February 23, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (13)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (13)

February 20, 2026
Next Post
SASSANYAN AMINCI (5)

SASSANYAN AMINCI (5)

Comments 1

  1. hayatu nura says:
    6 months ago

    wslm idan harda gaske yayi wannan batanci to shine kawai akasheshi annabifa? (saww) ammaduk abinda kefaruwa shine wasu sukabada kofar hakan domin mutum yadogarada wata fahimta kai kuma kanazaginsa kokace ya kauce WA.ATASIMU BIHABLILLAHI JAMI.AN WALATAFARRAQU BILLAHI fadar allahce

    Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Muhammad Salissou Hamissou: Ta’aziyyar Ƙwararren Ɗan Jarida Mai Raya Al’adun Gargajiya

Muhammad Salissou Hamissou: Ta’aziyyar Ƙwararren Ɗan Jarida Mai Raya Al’adun Gargajiya

February 26, 2024
RAMADAN KARIM: 16-1447

RAMADAN KARIM: 16-1447

March 5, 2026
Taya Ni Mu Gyara: Kisan Baƙi Sai Gayya

Taya Ni Mu Gyara: Kisan Baƙi Sai Gayya

November 1, 2025
Mummunar Zanza-Zanga A Ƙasar Nepal

Mummunar Zanza-Zanga A Ƙasar Nepal

September 11, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)
  • RAMADAN KARIM: 16-1447
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (7)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

RAMADAN KARIM: 16-1447

Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)

March 5, 2026
RAMADAN KARIM: 16-1447

RAMADAN KARIM: 16-1447

March 5, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.