Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Tarihin Shekara Biyu: Waiwaye A Turbar Nasara


~~~~~~~
A ranar Alhamis 5-12-1442 (Hijriyya), 15-07-2021 (Miladiyya), Bashir Yahuza Malumfashi ya rubuta waƙe mai taken “ALHAMDU LILLAH” a sakamakon yadda ya samu nasara a Gasar Rubutattun Wakokin Hausa” da Sashin Hausa na Jami’ar Usman Ɗanfodiyo ya shirya. Shekara biyu ke nan da wannan biki, mu sake bibiyar wannan waƙe don ƙarin jamdala:
~~~~~~~
ALHAMDU LILLAH!
Allahu Ƙadiran nai shela,
Na yi godiya nai hailala,
Na yi salati ga Manzona!
Allahu Kai kake rayawa,
Kai ne wanda bai ƙarewa,
Ka ƙarfafa mani ƙalbina.
Ka kai ni Sakkwato shaidawa,
Ka ba ni hanzarin dubawa.
Na yi nasara ga muradina.
Na duba ko’ina sashina,
Ga sha’irai tuli sassana,
Sun ƙarfafa ni kan aikina.
Na ga malamai ‘yan baiwa,
Yakasai garin yana haskawa,
Furof Bunza ne alƙalina.
Na ga jarumin jarummai,
Dogon Shugaba Allah tammai,
Ɗan Bilbis kake yayana.
Na yaba mutan Sifawa,
Na faɗa ina ƙarawa,
Baicinku ya cikan hannuna.
Na leƙa gidan mashahurai,
Allah hana su mazurai.
Ɗanfodiyo kake Shehuna.
Muhammadu muna duba ka,
Sambo mun yi sauraronka,
Wali lafiya rakkon sha’irina.
Wagga nasara samowa,
Amsa gare ku sadaukarwa,
Jimilla gare ku ZUMAINA!
Na yi godiyar Allahna,
Na yi jinjinar Manzona,
Alheran su gangaro ruhina.
~~~~~~~
© Bashir Yahuza Malumfashi
Alhamis 5-12-1442 (Hijriyya)
15-07-2021 (Miladiyya)
~~~~~~~









![Lost Heritage Series #1 – Mazari [Spindle]](https://i0.wp.com/taskargizago.com.ng/wp-content/uploads/2023/09/FB_IMG_1695164994735.jpg?resize=120%2C86&ssl=1)


