JARUMAR TIKTOK BABIYANA TA KAI ƘARAR MUSULMIN AREWA GA TINUBU DA VDM
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Wata shahararriyar ‘yar TikTik da aka fi sani da laƙanin Sarauniya Babiyana, ta kai ƙarar Musulmin Arewa zuwa ga Shugaban Ƙasa Tinubu da kuma ɗan rajin kare haƙƙin ɗan Adam, VDM – Very Dark Man, inda ta ce ana cin zarafinta a Soshalmidiya.
Babiyana ta bayyana ƙorafinta ne ta hanyar wani faifan bidiyo, inda take kuka share-share da hawaye. Ta ce Musulmin Arewa sun takura wa rayuwarta, suna zagin ta, suna cin zarafin ta, saboda “kuskuren da na aikata guda ɗaya tun bara, inda wani faifan bidiyona na tsiraici ya ɓulla,” in ji ta.
Ta ce a halin yanzu tana cikin tsananin damuwa, ba ta barci isasshe, ba ta cin abinci sosai; al’amarin har yana neman taɓa mata ƙwaƙwalwa.
“Musulmin Arewa, laifin me na yi maku, kuke uzura mani? Shin haka addininku ya koya maku? Haka Manzon Allah (saw) ya ce ku yi wa ɗan uwanku Musulmi idan ya aikata kuskure?

“Yaya kuke so in yi da rayuwata? Kuna son in kashe kaina ne?” In ji Babiyana, a lokacin da take neman Shugaba Tinubu da VDM su bi mata haƙƙinta.
Jama’a, mene ra’ayinku game da wannan ƙorafi na Babiyana? Kuma wace shawara za ku ba ta game da wannan hali da ta samu kanta?













