Daga Wakilinmu
A ranar Alhamis da ta gabata, Hukumar EFCC ta maka wasu manyan jami’an gwamnati biyu a gaban kotu, bisa zargin su da wawushe Naira miliyan 289 daga baitulmalin Gwamnatin Jihar Katsina.
An gurfanar da jami’an biyu, Sa’adu Maiwada da Sani Lawal BK gaban Mai Shari’a Musa Ɗanladi Abubakar bisa tuhumar su da aikata laifuka guda biyar, waɗanda suka haɗa da Haɗin Baki don aikata laifi da Zamba Cikin Aminci.
Wakilinmu ya kalato daga Babbar Kotun Jihar Katsina cewa, waɗanda ake tuhumar sun zabtare adadin kuɗin ne daga Baitulmalin Gwamnatin Jihar Katsina ta hanyar amfani da asusun ajiya na Kamfanin Integrated Gas Services Ltd. Katsina, inda shi Maiwada yake aiki a matsayin Darakta.
Hukumar EFCC ta bayyana cewa an tura adadin Naira miliyan 48 daga asusun ajiya na Kamfanin Integrated Gas Services Ltd zuwa asusun ajiyar banki mallakin Lawal BK, wanda a halin yanzu shi ne Mataimakin Babban Akanta na Jihar Katsina.
Sai dai dukkan waɗanda ake tuhumar sun musanta aikata laifin, inda Lauya mai gabatar da ƙara, A’isha Tahar Habib ta buƙaci kotu ta saka ranar ci gaba da sauraren ƙarar. Haka kuma Lauyan waɗanda ake tuhuma, J.B. Israel ya buƙaci a ba da belin su.
Mai Shari’a Ɗanladi ya amince da bayar da belin mutanen biyu bisa Naira miliyan biyar-biyar kowannensu. Sannan kuma ya ɗage sauraren ƙarar zuwa ranar 24 ga watan gobe.












