ƊAN BELLO
Tambarin Gwagwarmaya

__________
Wannan ƙasida daga Bashir Yahuza Malumfashi, sadaukarwa ce ga zaƙaƙurin ɗan gwagwarmayar tabbatar da mulkin gaskiya da adalci a Nigeria, Bello Galadancih, wanda aka fi sani da laƙanin Dan Bello.
__________
Ya Allahu, ga ni gare ka.
Na sallama kaina, a bautarka.
Na yabi Manzo, Badadinka.
Baban Fatima, ‘yar gatan Makka.
Roƙo a gare ka, ba zan gajiya ba.
Nai nufin kirari da muryata.
Wani gwarzo mai kishin ƙasata.
Ba ya gajiya wurin sassaita,
Al’amurra, bankaɗo zaluman ƙasata.
Wannan gwarzo, ba za ka ji kunya ba.
Malam Ɗan Bello, kana burge ni.
Bello Galadanchi, kai nai nufi ni.
Kai ke tsage gaskiya a ƙasar ni.
Zalunci ƙarara, duk ya firgita ni.
Jinjina a gare ka, ba zan fasa ba.
Mulaka’un ƙasarmu sun raina mu.
Sun mallake komai, suna dukan mu.
Sun raba kawuna, don su k+she mu.
Sun jirkita komai, har ma addininmu.
Shin hauka ake, a ce ba zan koka ba?
Sun zare subsidy a man gadonmu.
Sun maka haraji a dukkan lamurranmu.
Sun ƙukunce ‘yan adawa a ƙasarmu.
Ga shi sun bari ana ta k+she mu.
Shin jama’a, wai ba za mu farka ba?
Wai! A yau talaka ya bani.
An mai da shi ɗan-ba-ni-ba-ni.
An rarraba shi a sansani,
Cikin talauci da tsanani.
Lallai kam, ba za mu yafe ba.
Yau mulaka’u, kunya ta ƙaurace su.
Ba su san ta ba sam, rayuwarsu.
Cin amana, shi ne muradinsu.
Sai firgici, shi ne ruwan shan su.
Sun bar Allah, ba za su gane ba.
Dukiyar ƙasarmu, sun kwashe ta.
Sun rarrabe sassa, ko ko dukkanta.
Ga iyalai da karuwansu kwata.
Sun bi ƙasar, sun rarake ta.
Ba su san mutuwa na nan zuwa ba.
Ciwon kansu, sun ruga Ingila.
Ko ko Jamus, Faransa suna jigila.
Bikinsu ko bushasha, sai su shilla.
Dubai ko Amurka, ka ji gilla.
Ba su san hisabi na nan zuwa ba.
Masu mulki da attajiranmu,
Sun kashe ilimi a ƙasarmu.
Yara sai ragaita a titunanmu.
Babu aiki, ba sana’a garinmu.
Shin jama’a, ba za mu miƙe ba?
Sun ɗaukaka mawaƙi da Naira.
Ga Farfesa, an bar shi tsirara.
Gidansa, ruwan talauci ke kwarara.
Ɗalibai, an saka su fitsara.
Kaiconmu, in ba mu buɗe ido ba.
Ya ku jama’a, lallai mu tashi!
Mu ɗau aniya, babu fashi.
Mu ceto ƙasa daga ‘yan fashi.
Mu zaƙalƙale aiki da kishi.
‘Yancin ƙasarmu ba zai rushe ba.
Ku zo mu jera SABUWAR TAFIYA!
Ga Malam Bello mai aniya,
Da kyawun ƙuduri, gangariya.
Ku mu kamo rago, mu ƙyale akuya.
Nasararmu kam, ba za ta gaza ba.
Ya Allahu, ka ga ƙasarmu.
Ka ga yadda suka kassara mu.
Sun ƙwace komai, mallakarmu.
Sun murƙushe duk yunƙurinmu.
Kukanmu gare ka, ba za mu gaza ba.
Allah ka ceto mana ƙasarmu.
Ka yassare dukkan rayuwarmu.
Ka magance zaluncin nahiyarmu.
Ka murƙushe dukkan azzalumanmu.
Ka share hawayenmu, ya Rabba!
__________
© Bashir Yahuza Malumfashi
Juma’a-Eidil Kabir
10-12-1446 (Hijiriyya)
06-06-2025 (Miladiyya)
__________












