Shin Wai Akwai So? (1)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

A kwanakin baya, mun gabatar da muƙala, inda muka amsa tambayar ma’anar so, inda a ƙarshe muka yi tambayar cewa; shin akwai so, ko kuwa dai tunanin mutum ne kawai yake haska batun so a zuciya? To, a yau idan Allah ya yarda, za mu amsa wannan tambaya.
Tun da farko dai, ya kamata mu numfasa, mu yi tsam da ranmu sannan mu zurfafa tunani. Mu yi amfani da tunanin zuciyarmu da ƙwaƙwalwarmu domin amsa wannan tambaya, tun kafin ma mu nemi ƙarin bayani daga masana da magabata. Kuma babu shakka, mu shaida ne, cewa lallai akwai so kuma yana yin tasiri a rayuwarmu.
Dalili ke nan ma muke saka masoyanmu a zukatanmu, muke tarayya da su a cikin lamurranmu na rayuwa. Saboda akwai so, shi ya sa muke ji a ranmu cewa muna son wane ko wance. Muna ƙin wane ko wance.
Saboda akwai so, shi ya sa muke auren wane ko wance kuma muke ƙin auren wane ko wance. Saboda akwai so, shi ya sa muke sadaukar da kanmu ko abin hannunmu ga wane ko wance. Don haka, a bisa tunanin kanmu da nazarinmu, lallai akwai so!
To, bari kuma mu matsa gaba, domin tantance wannan tambaya. Shin me masana ko magabata suka ce? Manzon Allah, Muhammadu (saw) lallai ya tabbatar mana da cewa akwai so kuma akwai ƙi. Za mu gane haka ne ta hanyar bibiyar zantuttukansa da suka shafi lamarin so ko ƙi.
Hadisin Imam Bukhari, mai lamba 13 da na Imam Muslim, mai lamba 45, an ruwaito Manzon Allah (saw) yana cewa: “Ɗayanku ba zai kasance mai imani ba, har sai ya so wa ɗan uwansa, abin da yake so wa kansa.”
Daga wannan hadisi, za mu gane cewa, lallai akwai so. Abin da babu shi, babu yadda za a ce har Manzon Allah (saw) ya yi maganarsa.
A wani hadisin kuma, na Sahih Muslim, mai lamba 2566, Manzon Allah (saw) ya ce: “A Ranar Sakamako, Allah zai ce, ina waɗannan mutanen da suka so juna saboda girmana? Yau zan saka su cikin imuwata, ranar da babu wata inuwa sai dai tawa.”
Wannan babbar shaida ce da ke ƙara tabbatar mana cewa lallai akwai so, tun da Manzon Allah ya tabbatar mana da cewa Allah ya yi magana game da kalmar so.
Bari mu ƙara da Sunan Abi Dawud, hadisi mai lamba 5124, wanda aka ruwaito Manzon Allah (saw) yana cewa: “Idan wani ya ji a ransa cewa yana son ɗan uwansa, to ya sanar da shi cewa yana son shi.”
Ke nan ta tabbata akwai so, wanda kan ɗarsu a zukatan mutane. Wannan hadisi ya ƙara sanar da mu cewa mutum kan ji a ransa cewa yana son wani ko wata. Amsa dai ta tabbata, cewa lallai akwai wani abu mai suna so a rayuwar ‘yan Adam. Ga shi ma har Manzon Allah (saw) ya ba mu umurni da cewa, da zarar mun ji son wani ko wata ya kama mu, to mu sanar masa ko mata.
Jama’a, a nan za mu dakata, sai kuma a muƙala ta gaba, inda za mu tuntuɓi wasu masana, mu ji bayanansu kan cewa ko akwai so? Kafin sannan, ku shiga Comment Section, ku faɗa mana; shin ka taɓa kamuwa da son wata? Haka ke ma ‘yar uwa, kin taɓa son wani?
_______________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online)













