Tunawa Da Aboki Auwal Ɗanbarno
Daga Muhammad Lawal Barista

•••••••
A lokacin da wannan bawan Allah (Auwal Ɗanbarno) yake raye, ba ma ga maciji sam, ba ma iya zama a inuwa ɗaya, a fannin ra’ayi.
A mafi yawancin lokuta, duk abin da zai zo da shi, duk ingancinsa, zan bijire masa, kamar yadda shi ma, hakan yake yi a kaina, galibin lokuta. Amma fa abin da mutane ba su sani ba, ba ma haura mako guda ba mu haɗu ba. Idan har ban neme shi mun haɗu ba, to, shi zan neme ni.
Ya sha faɗa mani cewa yakan yi rubutu ya goge, ko ya yi ta gyare-gyare a kansa kafin ya sake shi, saboda gudun kar in kama shi a rubutun. Haka nan, yana haƙura da wani rubutun ma idan ya tuno ni, don ya san ba zan taɓa bari ba. Ni ma kuma haka abin yake a nawa ɓangaren. Idan kuma har ya zama dole sai ya yi rubutun, yana kira na a waya, ya ce don Allah kar in yi magana, akwai manufar da yake so ya cin ma wa a rubutun.
A iya tunanina, sau uku muka taɓa zama a inuwa ɗaya, kuma ra’ayi ɗaya a harkokin rubutu da marubuta. Na farko shi ne a 2005, yayin da aka yi taron marubuta na ƙasa a Jihar Kano, bayan tasowar wata turka-turka. Sai Kuma shekarar 2009, lokacin da na ce zan fito takarar Shugaban Ƙungiyar Marubuta ta Ƙasa, reshen Jihar Kano (ANA). Sai kuma a lokacin da muka yi wata haɗaka ta buga wani littafi, ni da shi da Kabiru Yusuf Fagge.
Na san wasu za su ce, to, mene ne asalin abin da ya haɗa mu, ya sa ba ma jituwa? Wannan kuwa dogon labari ne, da ba zai yiwu in kawo shi a wannan gajeren rubutu ba. A taƙaice dai, Auwalu Garba Ɗanborno, Babban Yarona (kamar yadda nake kiransa), mutumin kirki ne kuma mai damuwa da damuwar waɗanda yake tare da su.
Babu shakka, lokacin da labarin rasuwarsa ya riske ni, na yi matuƙar girgiza, don ko ba komai, na rasa abokin gwagwarmaya da fafatawa.
Ina roƙon Allah Ta’ala ya ji ƙan shi da rahama, ya haskaka kabarinsa, ya kyautata kwanciyarsa, ya yafe laifuka da kurakuransa, ya sanya aljannar Firdausi ce makomarsa. Amin-Summa-Amin!













