‘Yan Bindiga Sun Ɗauke Mahaifiyar Mawaƙi Rarara
Daga Wakilinmu

Kamar yadda masanin tsaro kuma Kakakin Ƙungiyar Jami’an Tsaron Sa-Kai Ta Najeriya, Malam Yahuza Ahmed Getso ya bayyana wa wakilinmu, wasu mutane da ake zargin ‘yan bindiga ne masu garkuwa da mutane domin amsar kuɗin fansa, da kimanin karfe 1.30 na daren jiya sun shiga garin Kahutu na Karamar Hukumar Ɗanja, sun ɗauke mahaifiyar shahararren mawaƙin siyasa, Alhaji Dauda Kahutu Rarara.
Kamar yadda ya ƙara bayani, ya ce ‘yan bindigar ba su yi harbi ba ko sau ɗaya, a yayin da suka shiga garin.
Haka kuma a makamancin wannan, wasu ‘yan bindigar da ake zargin ɓarayin shanu ne, da misalin ƙarfe 11:11 na daren na jiya, sun shiga ƙauyen Jinfin Idi (Gidan Barka) na Ƙaramar Hukumar Matazu, inda suka kori shanu tare da harbin wani mai suna Ya’u Jimfi, ɗan shekara 25 a ciki. Haka kuma suka sari wata mata mai suna Hussaina (Ushe) ‘yar shekaru 20 da wuƙa.
Sai dai kuma dakarun tsaro sun yi ba ta kashi da maharan, inda har suka samu nasarar kawar da ɗan bindiga ɗaya kuma suka ƙwato shanun da suka kora.













