KATSINA TA YI RASHI: Sa’in Katsina Ya Rasu

Allah Ya yi wa Sa’in Katsina, Alhaji Amadu Na Funtua rasuwa da safiyar yau Alhamis (21-12-1445 = 27-06-2024).
Marigayin ya rasu ne a Asibitin Koyarwa na Jihar Katsina, bayan jinya da ya sha.
Marigayin, wanda kafin rasuwar tasa shi ne Sa’in Katsina, mutum ne jajirtacce mai kishin al’umma. Ya kasance basarake mai muhibba kuma ɗan siyasa mai mutunci.
Allah Ya ji ƙan shi da rahama.













