Jami’an Tsaro Sun Ceto Ɗalibai da Malaman Oyo
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
__________
An kuɓutar da jimillar ɗalibai da malamai 44 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Oriire da ke Jihar Oyo, bayan wani gagarumin aikin tsaro na sama da wata guda da ya haɗa rundunonin tsaro da hukumomin leƙen asiri daban-daban na Najeriya.
An sace waɗannan ɗalibai da malamai ne a ranar 15 ga Mayu, 2026, kafin su samu ‘yanci a jiya Juma’a, 10 ga Yulin bana; sakamakon wani tsari na ayyukan tsaro da aka gudanar bisa ingantattun bayanan sirri domin rushe ƙungiyar ‘yan ta’addar da ta shirya sace su.
Babban Hafsan Runduna ta 2 ta Sojojin Najeriya da ke Ibadan (General Officer Commanding – GOC), Manjo Janar CR Nnebeife ne ya jagoranci wannan aiki tare da sauran hukumomin tsaro da suka gudanar da aikin cikin cikakkiyar haɗin gwiwa.

A cikin wata sanarwa da Muƙaddashin Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Runduna ta 2 ta Sojojin Najeriya, Laftanar Kanar Danjuma Jonah Danjuma ya fitar, ya bayyana cewa Sojojin Najeriya sun gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar rundunoni na musamman daga Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA), musamman Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC), Hedikwatar Tsaro ta Ƙasa, rundunonin musamman na Sojojin Ƙasa, Sojojin Ruwa da Sojojin Sama, Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya, Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), Hukumar Leken Asirin Waje ta Ƙasa (NIA), Hukumar Tsaron Fararen Hula ta Najeriya (NSCDC) da kuma jami’an sa-kai, mafarauta da ƙungiyar tsaron sa-kai ta Amotekun.
Sanarwar ta bayyana cewa jami’an tsaron sun gudanar da wani dogon aiki bisa bayanan sirri, wanda ya mayar da hankali wajen gano jagororin ƙungiyar ‘yan ta’addar da suka shirya satar, rushe tsarin ayyukansu, katse hanyoyin samar musu da kayan aiki da tallafi, tare da gano masu ba su bayanai da kuma maɓoyarsu.
“Mafi yawan waɗannan ayyuka sun gudana ne a cikin dajin Old Oyo National Park da ke Jihar Oyo, tare da bazuwa zuwa wasu jihohin ƙasar nan,” kamar yadda jam’in na hulɗa da jama’a ya bayyana.
A yayin gudanar da aikin, jami’an tsaro sun kama mutane da dama a Jihar Oyo da wasu sassan Najeriya. A cewar sanarwar, “jami’an tsaron sun tarwatsa tsarin ƙungiyar, sun raunana ƙarfinta, tare da matsa mata lamba har ta kai ga sakin ɗaliban da malamansu, ba tare da wani sharaɗi ba.”
Mahukuntan soja sun bayyana cewa an tsara tare da aiwatar da aikin cikin matuƙar taka-tsan-tsan, domin kare rayukan waɗanda aka yi garkuwa da su da kuma kauce wa jikkata fararen hula.
Duk da nasarar da aka samu wajen ceto mutanen, sanarwar ta bayyana cewa wasu jami’an tsaro sun rasa rayukansu ko suka jikkata yayin gudanar da aikin, abin da ke nuna irin sadaukarwar da suke yi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
A halin yanzu, ɗaliban da malamansu da aka kuɓutar suna karɓar kulawar likitoci a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba, inda ake duba lafiyarsu tare da ba su magani. Ana sa ran daga baya za a miƙa su ga Gwamnatin Jihar Oyo, domin haɗa su da iyalansu.
Da yake yabawa da nasarar aikin, Manjo Janar CR Nnebeife ya miƙa godiyarsa ga Shugaban Ƙasa kuma Babban Kwamandan Rundunonin Sojojin Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, bisa jagoranci, goyon baya da kuma samar da dukkan abubuwan da suka taimaka wajen samun nasarar wannan aiki. Haka kuma ya gode wa Gwamnan Jihar Oyo, Injiniya Seyi Makinde da al’ummar jihar bisa ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai tun daga farkon lamarin har zuwa ƙarshe.
Babban Hafsan Rundunar ya kuma yaba wa Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, Ministan Tsaro, Babban Hafsan Tsaro, Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, sauran Shugabannin Rundunonin Tsaro, Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Daraktocin Janar na DSS da NIA da shugabannin sauran hukumomin tsaro, bisa kyakkyawae haɗin kai da suka nuna, wanda ya tabbatar da gudanar da aikin cikin tsari da nasara.
Har ila yau, ya gode wa kafafen yaɗa labarai da daukacin ‘yan Najeriya saboda haƙuri, fahimta da kuma ci gaba da nuna amincewa da tsarin tsaron ƙasa. Ya buƙaci jama’a su ci gaba da kasancewa cikin shiri, tare da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanan sirri cikin lokaci; domin ƙarfafa ƙoƙarin da ake yi na kare rayuka da dukiyoyi a faɗin Najeriya.
Nasarar wannan aiki na ceto na daga cikin manyan nasarorin haɗin gwiwar hukumomin tsaro da aka samu a baya-bayan nan kuma hakan ya sake nuna muhimmancin amfani da ingantattun bayanan sirri da haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran manyan laifuka a Najeriya.
Mahukunta sun bayyana cewa za a ci gaba da gudanar da wasu ƙarin ayyuka, domin kamo sauran ‘yan ta’addar da ke da hannu a wannan aika-aika tare da hana aukuwar irin waɗannan hare-hare a nan gaba.
__________













