PDP Ta Naɗa Yusuf Dingyaɗi Sabon Muƙami
Jam’iyyar PDP ta Ƙasa ta bayyana naɗin Malam Yusuf Abubakar Dingyaɗi a matsayin wakili a cikin Kwamitin Musamman da zai lura da harkokin hulɗa da ‘yan jarida da watsa labarai na zaɓen gwamnoni a jihohin Bayelsa da Kogi da Imo, wanda ake sa ran gudanarwa a tsakanin watanin Nuwamba da Disamba masu gabatowa, kamar yadda Babban Sakataren Watsa Labarai na Jam’iyyar PDP na Ƙasa, Mista Debo Olugangba ya sanar wa manema labarai.
Haka ma jam’iyyar ta PDP ta bayyana sunayen sauran wakilai guda 19, waɗanda suka ƙunshi, Sakataren Watsa Labarai na PDP na Ƙasa; Mista Debo Ologunagba, a matsayin Shugaba da Mista Richard Ihediwa, wanda zai kasance Sakatare. Sauran membobin sun haɗa da Mista Kola Ologbondiyan da Emmanuel Ibeshi da Ibrahim Abdullahi da Otunba Segun Sawunmi da Osaro Onaiwu da Abdul M. Bashir da sauransu.
Malam Yusuf Dingyaɗi, wanda shi ne Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa (SSA) a kan Watsa da Sadarwa, ya taɓa riƙe muƙamin Mataimakin Daraktan Labarai da ‘Yan Jarida na kamfen ɗin Atiku/Okowa a yankin Arewa a zaɓen da ya gabata.
Ana sa ran ƙaddamar da wannan kwamitin na mussaman a Abuja, nan gaba kaɗan.












