Janar Faruk Yahaya Ya Zama Zaruman Sakkwato


A ranar Asabar da ta gabata (12-08-2023), Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Sultan Sa’adu Abubakar ya naɗa Laftanar-Janar Faruk Yahaya (mai ritaya), CFR, Sarautar Zaruman Sakkwato.
Bayan naɗin nasa, al’ummar Jihar Sakkwato sun shirya masa gagarumar daba, domin taya shi murnar kammala aikin soja lami lafiya, cikin gagarumar nasara. Janar Faruk ya kammala aikinsa na soja a ranar 23-06-2023, bayan ya kwashe kimanin shekara 37 a fagen aiki. Ya kammala aiki ne da muƙamin Laftanar-Janar, sannan kuma a matsayin Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Nigeria.
Da yake bayyana kyawawan halayensa sabon Zaruman Sakkwato, Babban Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojojin Nigeria, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya ce: “Shi mutum ne mai ƙana’a, jajirtacce, mai ƙaunar ƙasarsa ta haihuwa. A kullum idan yana bakin aiki, yakan nuna sadaukarwa da nuna ƙwazo da himma. Waɗannan kyawawan halaye nasa ne suka taimaka masa har ya cin ma ɗarewa ƙololuwar muƙami a Gidan Sojojin Nigeria, inda kuma ya zama Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Nigeria na 22.”
A yayin gagarumar dabar da aka shirya masa kuwa, Aal’ummar Jihar Sakkwato sun fito ƙwansu da kwarkwata. Manya da matasa, wasu a kan dawakai da raƙuma, wasu a kan motoci da babaura, wasu ma a ƙasa suka yi wa Babban Filin Wasanni na Sakkwato tsinke, ɗaliban makarantu daban-daban da makaɗa da mawaƙa suka gudanar da wasannin gargajiya domin karrama shi da yi masa barka da arziki.
Shugaban Kwamitin da ya shirya wannan gagarumar Daba, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, ya yaba sosai da halayen Janar Yahaya. Ya ce shi shahararren mutum ne kuma abin alfahari, a matsayinsa na ɗan Sakkwato mai mutunci, wanda ya bayar da gagarumar gudunmowa ga ƙasarsa ta haihuwa da kuma Gidan Sojan Nigeria.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Sakkwato, Dokta Ahmad Aliyu Sakkwato, ya bayyana Janar Faruk a matsayin mutum mai riƙon amana, wanda za a yi ƙishirwar gudunmowarsa a Gidan Sojan Nigeria.
Shi kuwa magajinsa, Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Nigeria, Laftanar-Janar Taoreed Lagbaja, yaba wa Zaruman na Sakkwato ya yi, wanda ya ce shugabansa ne abin koyi a Gidan Soja. Ya ce ya bar babban gurbi mai wuyar cikewa a aikin soja. Ya ce ya bar babban tarihi da za a daɗe ana tunawa da shi a Gidan Soja.
Shi kuwa Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji (Dokta) Sa’ad Abubakar III CFR, ya ƙimanta shi da Shahararren Janar, wanda ya taka rawa abin yabawa a fagen yaƙi, mulki da kuma aiki ga al’ummarsa.
Zaruman Sakkwato, Janar Faruk Yahaya, an haife shi a garin Sifawa na Karamar Hukumar Boɗinga. Yana auren Hajiya Salamatu Faruk, wadda ta haifa masa kyawawan ‘ya’ya kuma ta riƙe shi da soyayya da zumunci a matsayinta na Uwargida.
Wasu daga cikin hamshaƙan mutane da suka halarci gagarumar Dabar karrama Zaruman Sakkwato sun haɗa da tsohon Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Nigeria, Laftanar-Janar Tukur Yusufu Buratai, CFR (mai ritaya), Betaren Biu, da Birgediya-Janar Sani Usman Kukasheƙa, mni (mai ritaya), Sarkin Yaƙin Kanwan Katsina da tsohon Ministan Harkokin ‘Yan Sanda, Alhaji Maigari Dingyaɗi da tsohon Shugaban Rundunar Tsaro, Janar Lucky Irabor (mai ritaya) da sauransu.














Allah Ya yi musu jagora Ya ba su ikon sauke nauyin da ke kansu. Shugabanci abu ne mai wahala duk da ya kai ƙololuwa a aikinsa na gwamnati.
Amin Amin Ya Allah. Babu shakka shugabanci babban al’amari ne.