TSOKACINMU NA YAU – 01
Yau Asabar, 01-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 01-Maris-2025 Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya kai ɗan uwa, ka natsu, ka yi tsam da ranka, ka yi tunani. Kai fa mutum ne ɗan Adam, wanda Allah Ya halitta daga ruwa da yumɓu, Ya busa maka rai kuma Ya sanya maka tunani, domin bambance fari da baki – abu mai kyau da gurɓatacce. Don haka, duk abin da za ka aikata, ka aikata shi da tunanin cewa kai fa mutum ne, wanda zai mutu kuma zai fuskanci hisabi.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













