
Mataimaki Na Musamman ta fuskar Watsa Labarai ga tsohon Ministan Tsaro, Manjo-Janar Janar Bashir Magashi (mai ritaya), Mohammed Abdulkadir ya bayyana cewa babu ƙanshin gaskiya da labarun da ke yaɗuwa na cewa tsohon Ministan ya rasu.
Sai dai kuma wani bincike ya tabbatar da cewa an samu kuskure ne waje yaɗa labarin ba tare da tantancewa ba, Kasancewar wani bawan Allah ne mai suna Dokta Labaran Kabir Magashi ya rasu da safiyar Talatar da ta gabata a Kano. An samu kuskure ne daga masu ba da labarin, saboda sunan Magashi da ke jikin sunan mamacin, wanda ya yi kama da na Minista.
Da yake bayani game da lamarin, Janar Magashi ya yi addu’ar Allah ji ƙan mamacin, sannan kuma ya yi godiya ga ‘yan uwa da abokan arziki da al’ummar Najeriya da suka yi ta tuntubar shi ta waya, domin nuna alhininsu kan lamarin.













