Madakin Zazzau Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Hakimin Basawa
Madakin Zazzau, tsohon Daraktan Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa na Nigeria, Alhaji Muhammadu Munnir Ja’afaru ya ajiye muƙaminsa na Hakimin Basawa a Masarautar Zazzau.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, sanarwar ajiye muƙamin ta fito ne daga Abdullahi Aliyu Ƙwarbai, Jami’in Watsa Labarai na Masarautar Zazzau, wanda ya bayyana cewa tuni Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya amince da saukar tasa, har ma ya naɗa wani Hakimin ya maye gurbinsa.
“Dangane da samun wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 29 ga Yuli, 2023 daga Madakin Zazzau, Alhaji Muhammadu Munnir Ja’afaru, Hakimin Basawa, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli CFR, LLD ba tare da ɓata lokaci ba, ya amince da naɗin Architect Haruna Abubakar Bamalli, Barde Ƙerrariyyan Zazzau, Hakimin Zangon Aya a matsayin Hakimin Basawa,” kamar yadda Jami’in Watsa Labaran Masarautar Zazzau ya bayyana.













