• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, May 2, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

A Mako Ɗaya Kacal: Jami’an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria

Ciki Har Da Lauya Da Ɗalibin Da Zai Je Turai

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
July 17, 2023
in Babban Labari
0
A Mako Ɗaya Kacal: Jami’an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria
48
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

A Mako Ɗaya Kacal: Jami’an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026

Jami’an Hukumar Yaƙi Da Tu’ammali Da Muggan Ƙwayoyin Ta Ƙasa (NDLEA) sun yi nasarar kama wani ɗalibi ɗan shekara 19, Benjamin Nnamani Daberechi, a Filin Jirgin Saman Ƙasa-da-Ƙasa na Nnamdi Azikiwe, Abuja, Nigeria, da ƙunshin ƙwayar methamphetamine mai nauyin kilogiram 7.2, da aka ɓoye a kwandon kifin miya, a yayin da yake ƙoƙarin fita da ita zuwa Turai, inda zai je ɗalibta.

Da yake bayyana waɗannan nasarori da hukumar ta samu ga ‘yan jarida, Daraktan Watsa Labarai Da Wayar Da Kan Jama’a na NDLEA, Mista Femi Babafemi ya ce jami’an nasu sun kama matashin ne a ranar Laraba da ta gabata (12-07-2027), a yayin da ake tantance fasinjojin da za su shiga jirgin Turkish Airlines mai lamba TK0624. Da farko an tambayi matashi Daberechi inda za shi, ya amsa da cewa zai je karatu ne ƙasar Cyprus amma da aka tsananta bincike a jikkarsa, sai aka gano ƙullin farin maganin mai nauyin kilogiram 7.2, a ɓoye cikin kifin miya. Bayan an auna da na’ura, sai aka samu tabbacin cewa muguwar ƙwayar Methamphetamine ce.

Ya ce haka kuma, jami’an na NDLEA da ke aiki a Mashigar Ruwa ta Tincan, sun sake samun nasara a ranar Talata da ta gabata (11-07-2023), inda suka kama tabar wiwi mai nauyin kilogiram 116.5, wacce aka ɓoye cikin jakunkuna, ƙasan ƙarafunan mota, a cikin kwantena mai lamba FCIU 8459700, wacce ke ɗauke da gwanjon motoci uku da aka shigo da su daga birnin Toronto na ƙasar Canada.

“Tsattsauran binciken haɗin gwiwa tsakanin jami’an NDLEA da Kwastam da DSS ne ya tabbatar da cewa, lallai waɗannan ƙunshi 233 da aka ɓoye cikin ƙarafunan mota, tabar wiwi ce,” in ji Darakta Femi.

Ya ci gaba da bayyana cewa, baya ga wannan nasara, a karo daban-daban, jami’an na NDLEA da ke Aikin Bincike Da Gudanarwa a Lagos sun daƙile wasu ɓata-gari da suka so shigo da ganyen wiwi ta hanyar amfani da kamfanonin aika saƙonni. A kan haka suka taɓa kama giram 336 na ganyen da aka ɓoye cikin na’urar kwamfutoci za a fita da su zuwa Dubai, suka kama mutumin da ake zargi, Ibrahim Analu, ɗan shekara 28, a Tashar Motar Iddo, Lagos, a yayin da yake shirin aika adadin wasu muggan ƙwayoyin guda 151,700 zuwa Kaduna. Haka kuma sun sake bankaɗo wani ƙullin ganyen wiwi mai nauyin kilogiram 4.830 a wani kamfanin aika saƙonni, a wani jirgin ruwa da ya zo Nigeria daga birnin Douala na ƙasar Cameroon, zai wuce ƙasar Oman. An ɓoye ƙunshin ganyen ne cikin gwangwanaye 10 da ke ɗauke da tsimin gargajiya da ake kira da laƙanin Banga. Dukkansu an sanya su cikin wani katan.

A bayanin nasa ga ‘yan jarida, Femi ya ce: “Jami’anmu kuma sun yi nasarar cafke wata lauya da ke da zama a Unguwar Lekki, Lagos, mai suna Ebikpolade Helen, wacce ta ƙware a sana’ar haɗa abin sha da muggan ƙwayoyi. An kama ta ne a garin Awka na Jihar Anambra, inda dama an taɓa kama kilogiram 5 na tabar wiwi da kwalabe 12 na haɗin muggan ƙwayoyi a gidanta da ke unguwar ta Lekki.”

Wata nasarar da NDLEA ta samu a ranar Alhamis da ta gabata (13-07-2023), kamar yadda Darakta Femi ya bayyana, ita ce kama wani mai suna Abubakar Shuaibu, a Unguwar Cappa, kan titin Mushin/Oshodi da kwalabe 86 na sinadarin Kodin, mai awon lita 8.6, a cikin motarsa ƙirar bas Toyota mai lamba FFA 241 YB. An kama wasu ƙarin mutum biyu da ake zargi, Razak Ogunbo da Adeola Idowu a ranar Talata (11-07-2023) a Unguwar Ikorodu da lita 51 na lamurjen muggan ƙwayoyi. Kamar kuma yadda a ranar Laraba (12-07-2022) aka kama kilogiram 372 na tabar wiwi da kwalabe 48 masu adadin lita 48 na lamurjen muggan ƙwayoyi a gidan wani dilan muggan ƙwayoyi da ya tsere Unguwar Akala da ke Mushin a Lagos.

A jihar Ondo kuwa, jami’an NDLEA wani gida suka fafara, a Unguwar Ehin-Ala, Ƙaramar Hukumar Akure ta Kudu, inda aka cafke wani Abubakar Zayyanu Gyambar, mai shekara 28. An same shi da manyan jakunkuna masu nauyin kilogiram 1,944 na tabar wiwi. Inda kuma shi wani da ake zargi, Henry Wilson, mai shekara 50, aka kama shi a garin Ogume na Ƙaramar Hukumar Ndokwa ta Yamma, Jihar Delta da irin wannan taba mai nauyin kilogiram 216.5.

A Arewa kuwa, an kama tabar wiwi mai nauyin kilogiram 45.41 a hannun Adam Hassan, mai shekara 27 a kan hanyar Ingawa-Mani-Mashi, a Jihar Katsina, yana zuwa Jamhuriyar Nijar.

“An kama kilogiram 70 na wani sinadari daga hannun Mamman Nur Shettima, a ranar Asabar (15-07-2023), a kan hanyar Kano zuwa Nguru, Jihar Yobe.”

A Jihar Kano, an kama wani Abdulhamid Lawan Bayero, mai shekara 48, a ranar Juma’ar da ta gabata, a Unguwar Ɗan Agundi da sunƙin tabar wiwi 114, mai nauyin kilogiram 71.7. A daidai lokacin kuma aka kama ƙwayoyin Tamol (Tramadol) guda 50,000 a Ƙofar Waika.

Darakta Femi ya sake bayyana wata babbar nasarar da NDLEA ta samu a ranar Alhamis da ta gabata, inda suka kama muggan ƙwayoyi guda 912,600, ciki har da Tramadol a wasu motocin haya biyu, ɗaya daga Lagos za ta Kano, aka kama ta a titin Abuja-Jere-Kaduna. Wanda aka kama shi ne Sahabi Lawal mai shekara 25.

A Jihar Borno kuwa, nan ma jami’an na NDLEA ba su yi ƙasa gwiwa ba, domin kuwa a cewar Femi, sun kama Umar Tijjani Mustapha, mai shekara 32 a Gangamari, ɗauke da kilogiram 55.25 na tabar wiwi, duk a ranar Alhamis da ta gabata.

Da yake jinjina wa jami’ansa, bisa namijin ƙoƙarin da suka nuna, Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya-Janar Buba Marwa (mai ritaya) ya yaba wa jajirtattun jami’an hukumar da ke Filin Jirgin Saman Ƙasa-da-Ƙasa na Nnamdi Azikiwe Abuja da na Tincan, Lagos, Ondo, Katsina, Yobe, Delta, Kano, Kaduna da Borno da kuma Sashin Gudanarwa da Bincike da ke Lagos da kuma dukkan jami’ai da ke sassan ƙasar nan.
“Lallai ku ƙara zage damtse ku kula,” inji Shugaba Marwa.

Previous Post

₦8000 Ba Za Ta Sayi Tiyar Masara 10 Ba – Sarkin Samarin Galadima

Next Post

Za Mu Tunkari Matsalolin Ruwa Da Gaske A Jihar Katsina – Injiniya Tukur

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume
Babban Labari

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel
Babban Labari

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

April 2, 2026
Next Post
Za Mu Tunkari Matsalolin Ruwa Da Gaske A Jihar Katsina – Injiniya Tukur

Za Mu Tunkari Matsalolin Ruwa Da Gaske A Jihar Katsina - Injiniya Tukur

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

SAƘON JUMU’A: Daga Malam Anas Saminu Ja’en

SAƘON JUMU’A: Daga Malam Anas Saminu Ja’en

October 6, 2023
Jihar Katsina Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Daminar Bana

Jihar Katsina Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Daminar Bana

July 9, 2023
Rai Baƙon Duniya: Allah Ya Ji Ƙan Abokinmu Yahaya Skito

Rai Baƙon Duniya: Allah Ya Ji Ƙan Abokinmu Yahaya Skito

November 15, 2025
JIHAR KATSINA/MALUMFASHI MUN YI BABBAN RASHI

JIHAR KATSINA/MALUMFASHI MUN YI BABBAN RASHI

February 24, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.