• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, March 5, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Sharhi

Gwamnatin Kano: Rushe Gidajen Mutane Zalunci Ne

Babu Adalci A Rushe-Rushe

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 17, 2023
in Sharhi
0
Gwamnatin Kano: Rushe Gidajen Mutane Zalunci Ne

Gidajen da ake son rusaw

84
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Daga Adam Ahmad Muhammed

A yau zan yi tsokaci a kan filin Polytechnic da aka wayi gari ‘yan rusau sun dirar masa.

Related posts

SHEIKH YAKUBU YAHAYA KATSINA: ZUWAN KA TA’AZIYYAR BUHARI KOYI NE DA HALAYEN MANZON ALLAH (SAW)

SHEIKH YAKUBU YAHAYA KATSINA: ZUWAN KA TA’AZIYYAR BUHARI KOYI NE DA HALAYEN MANZON ALLAH (SAW)

July 18, 2025
Sharhin Littafin Faɗakarwa Dangane Da lllar Miyagun Ƙwayoyi

Sharhin Littafin Faɗakarwa Dangane Da lllar Miyagun Ƙwayoyi

December 24, 2024

Da farko dai Ganduje bai kyauta ba da ya yanka filayen ya rabar, ko ni a lokacin ban goyi baya ba.

Zan iya tunawa har Daraktan Makarantar aka cire daga kujerarsa don kawai ya ce bai ga dacewar karɓe wa makarantar wannan fili ba.

Duk da cewa shi Daraktan ya san Gwamna Ganduje ya bayar da wani katafaren filin a Badume, wanda ya fi wannan girma nesa ba kusa ba.

A ra’ayin Daraktan shi ne, kamata ya yi a ce wancan na Badume ƙari ne ga makarantar ba wai canji ba.

A kan wannan ra’ayi nasa ne ake ganin ya yi fito na fito da ra’ayin gwamnati, duk da cewa ba wai a bainar jama’a ya yi maganar ba, ya yi maganar ce a WhatsApp Group na abokan aikinsa.

A haka dai aka cire shi kuma aka yanka filayen aka raba wa ‘yan gata.  Tabbas babu mai kishin da zai goyi bayan wannan aiki.

An raba filaye bisa tsarin gwamnati. Mafi yawa da aka bai wa sayarwa suka yi, waɗanda suka saya kuma suka bi ƙa’idoji suka gina kayansu. Ni dai a nan ban ga laifinsu ba, tun da dai a doka Gwamna yana da ikon yin haka.

A yanzu kuma an sami sabon Gwamna da yake ganin hakan ba daidai ba ne, kuma yake ganin rushe wajen shi ne kawai hanyar bi.

A ra’ayina wannan mataki ba daidai ba ne, kamata ya yi idan har ta kama dole sai an ƙwace filayen, to a bi hanyar doka, a biya masu gidajen diyya, saboda dai ba ‘yan share wuri zauna ba ne.

Ko bayan an biya su diyya bai kamata a rushe gidajen ba, sai a duba idan akwai abin da za a iya amfani da su sai a yi.

Idan kuma Gwamna yana tsoron kada a tsaya bin doka a ƙarshe a tabbatar musu da gigajen ne ya sa yake rushewa, to an kuma.

Idan har akwai yiwuwar wata doka ko hukuma za ta iya mallaka musu filayen, to gara a bari ta mallaka musu din. Saboda wannan rushewar da ake yi, rushe tattalin arzikin Kanawa da Kano ne. Idan ana ganin wai an ƙwato wa Kanawa filinsu ne, to Kanawa dai aka kashe wai don a ƙwato wa Kanawa da Kano fili.

Duk wanda ya san ciwon dukiya da muhimmancin kuɗi a rayuwar nan zai ji ciwon yadda ake rusa dukiya ba gaira ba dalili. Idan da za ka ji biliyoyin da ake yi wa mutane asara da kanka ba zai iya ɗauka ba.

To kuwa meye hikimar a yi asarar irin wannan dukiya don kawai ana tunanin idan an ƙwace wata kotu ko wata gwamnati za ta iya dawo musu da gidajensu?

Duk wanda ka ga yana murnar wannan abin da ake yi to irin matsiyatan da suka tashi cikin taluci ne, ba su san wani abu arziki ba. Su so suke yi a karya duk wani mai arziki ya dawo kamar su.

Wannan dai kawai ra’ayinane ba shawara ba, saboda su sun ce ba sa buƙatar shawarar kowa da ba a cikinsu yake ba.

Allah Ya raba mu da aikin mai hassada a yayin da ya yi hassadarsa.


Malam Adam Ahmad Muhammed, Daga Jihar Kano.

Previous Post

Da Sun Ce Tsohon Nan Auduga Ne

Next Post

Ba Za Ku Yi Nadamar Zaɓen Mu Ba

Related Posts

SHEIKH YAKUBU YAHAYA KATSINA: ZUWAN KA TA’AZIYYAR BUHARI KOYI NE DA HALAYEN MANZON ALLAH (SAW)
Sharhi

SHEIKH YAKUBU YAHAYA KATSINA: ZUWAN KA TA’AZIYYAR BUHARI KOYI NE DA HALAYEN MANZON ALLAH (SAW)

July 18, 2025
Sharhin Littafin Faɗakarwa Dangane Da lllar Miyagun Ƙwayoyi
Sharhi

Sharhin Littafin Faɗakarwa Dangane Da lllar Miyagun Ƙwayoyi

December 24, 2024
SAI AN YI DA GASKE: Littafin Wasan Kwaikwayo A Mizanin Nazari Da Sharhi
Sharhi

SAI AN YI DA GASKE: Littafin Wasan Kwaikwayo A Mizanin Nazari Da Sharhi

November 16, 2023
Next Post
Ba Za Ku Yi Nadamar Zaɓen Mu Ba

Ba Za Ku Yi Nadamar Zaɓen Mu Ba

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Gwamnati Ta Kula Da Mu

Gwamnati Ta Kula Da Mu

May 29, 2023
Ɓarayin Fetur Sun Kwashi Kashinsu A Hannun Sojojin Najeriya

Ɓarayin Fetur Sun Kwashi Kashinsu A Hannun Sojojin Najeriya

June 27, 2023
TAURARON GIZAGO: Idris Ibrahim Kubau

TAURARON GIZAGO: Idris Ibrahim Kubau

August 13, 2023
Maraba Da Sabon Gidan Rediyon Afirka

Maraba Da Sabon Gidan Rediyon Afirka

October 8, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)
  • RAMADAN KARIM: 16-1447
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (7)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

RAMADAN KARIM: 16-1447

Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)

March 5, 2026
RAMADAN KARIM: 16-1447

RAMADAN KARIM: 16-1447

March 5, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.