• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, July 10, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
February 26, 2026
in Babban Labari
0
Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

Daga sama, Walida Abdulhadi Ibrahim ce da jaririyarta, a ƙasa kuma Gwamnan Jihar Jigawa ne, Alhaji Umar Namadi

108
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

ACF Endowment Fund Sets Agenda for Transparency, Education and Empowerment in Northern Nigeria

Asusun Tallafi na ACF Ya Tsara Sabuwar Hanyar Bunƙasa Ilimi da Ƙarfafa Al’ummar Arewa

June 25, 2026
Matasa Masu Fusata Sun Ƙone Ofishin ’Yan Sanda

Matasa Masu Fusata Sun Ƙone Ofishin ’Yan Sanda

June 20, 2026
Daga sama, Walida Abdulhadi Ibrahim ce da jaririyarta, a ƙasa kuma Gwamnan Jihar Jigawa ne, Alhaji Umar Namadi

 

__________

Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, a daren jiya Laraba ya karɓo Walida Abdulhadi Ibrahim daga hannun Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) da ke Abuja.

Walida dai ta jima a hannun Hukumar ta DSS, wacce take binciken jami’inta mai suna Ifeanyi, wanda ake zargin ya sace ta daga Jigawa, ya tilasta mata shiga addinin Kirista, sannan kuma ya yi mata ciki har ta haifi jaririya, ba tare da sanin iyayenta ba.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, a yayin da Gwamna Namadi ke ƙarin bayani game da batun, ya ce batutuwan da suka shafi sace Walida, za a bar su ga kotu ta warware, yana mai tabbatar da cewa za a yi adalci a kan batun.

Gwamnan ya ce Walida ‘yar Jihar Jigawa ce kuma gwamnati za ta tabbatar da tsaron lafiyarta tare da cikakkiyar murmurewarta daga duk wata damuwa ko tashin hankali da take fuskanta.

Gwamnan ya samu rakiyar Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Haruna Aliyu da Babban Lauya kuma Kwamishinan Shari’a, Barista Bello Abdulƙadir Fanini da Kwamishiniyar Harkokin Mata, Hajiya Hadiza Abdulwahab da takwaransa na Ma’aikatar Muhalli, Dakta Nura Ibrahim Doka da sauransu zuwa hedikwatar DSS da ke Abuja.

A nasa ɓangaren, Babban Daraktan Hukumar DSS, Adeola Oluwatosin Ajayi, tare da manyan jami’an hukumar ne suka miƙa Walida ga gwamnan. Sannan kuma ya ce wanda ake zargi da sace Walida, wato Ifeanyi, yana tsare a hannun hukumar, wadda za ta ci gaba da bincike har zuwa ƙarshe. Yana mai tabbatar da cewa muddin wanda ake zargi ya aikata laifin, to zai fuskanci hukunci a hannun Shari’a.

Ya zuwa yanzu dai, ƙungiyoyin ‘yancin ɗan Adam daban-daban da sauran al’umma sun zuba ido tare da kiran cewa lallai a yi wa yarinya Walida da iyayenta adalci. Suna masu buƙatar lallai a hukunta Ifeanyi bisa cin zarafinta da ake zargin ya aikata.

__________

Previous Post

RAMADAN KARIM: 09-1447

Next Post

…BUT WHERE IS IFEANYI?

Related Posts

ACF Endowment Fund Sets Agenda for Transparency, Education and Empowerment in Northern Nigeria
Babban Labari

Asusun Tallafi na ACF Ya Tsara Sabuwar Hanyar Bunƙasa Ilimi da Ƙarfafa Al’ummar Arewa

June 25, 2026
Matasa Masu Fusata Sun Ƙone Ofishin ’Yan Sanda
Babban Labari

Matasa Masu Fusata Sun Ƙone Ofishin ’Yan Sanda

June 20, 2026
Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar
Babban Labari

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

June 12, 2026
Next Post
…BUT WHERE IS IFEANYI?

...BUT WHERE IS IFEANYI?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

An Kafa Gidauniyar Danbarno

An Kafa Gidauniyar Danbarno

June 30, 2023
Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko

Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko

October 9, 2025
Ranar Dimokuraɗiyya: Mu Jajirce Wajen Gina Ƙasa – MD Abubakar

Ranar Dimokuraɗiyya: Mu Jajirce Wajen Gina Ƙasa – MD Abubakar

June 11, 2023
RAMADAN KARIM: 06-1447

RAMADAN KARIM: 06-1447

February 23, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana
  • Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage
  • Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

July 10, 2026
Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

July 9, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.