Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Sunansa Abraham Richmond. Shi babban Limamin Kirista ne a ƙasar Afirka ta Kudu. Bisa yardar Allah, sai ga shi ya amshi Musulunci. Ba shi kaɗai ba, har ma da dukkan mabiyansa, mutum sama da dubu 100.
A bana ya Musulunta kuma yana ɗaya da cikin Musulmi miliyan biyu da suka sauke farali a ƙasa mai tsarki a Hajjin bana.
A wasu rahotannin gaskiya da Taskar Gizago ta tantance, Malam Ibrahim ya musulunta ne a sakamakon wani mafarki mai ban al’ajabi da ya yi.
Kamar yadda ya shaida wa ‘yan jarida, ya ce yana barci ne sai ya ji wata murya a mafarki tana ba shi umurni da cewa: “Da kai da mabiyanka, ku sanya sutura irin ta Musulmi.”
Ya ce tun daga nan a kullum ya kwanta barci, sai ya maimaita wannan mafarki. A kowane lokaci kuma muryar da ke yi masa magana ƙarfi take ƙarawa. A kan haka, kawai sai ya ji ya samu natsuwar amsar Kalmar Shahada, ya shiga Musulunci.
Ya bayyana cewa, ya kwashe shekara 15 yana jagorantar mabiyansa a Addinin Kirista, kafin wannan al’amarin ya faru. Ya ce a lokacin da ya amshi Musulunci, sai ya sanya suturu irin na Musulmi kuma ya tunkari cocinsa a cikin wannan shiga.
“Da na shiga cocin, sai na shaida masu umurnin da aka ba ni a mafarki. Abin mamaki, babu wanda ya yi mani gardama. Su ma nan take suka amshi Musulunci,” in ji Alhaji Ibrahim Richemond.
A Hajjin bana, ba shi kaɗai ya samu damar sauke farali ba, domin kuwa akwai da yawa daga mabiyansa da su ma suka bi shi zuwa Saudiyya. Kuma sun samu gagarumar tarba da kulawa ta musamman

daga hukumomin Makka.
Ya canja sunansa daga Abraham zuwa Ibrahim kuma ya ziyarci dukkan muhimman wuraren tarihi da ke Saudiyya, inda a wasu wuraren har yana zubar da hawaye saboda shauƙin natsuwa da ya shiga zuciyarsa.













