Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano
Daga Wakilnmu

___________
Ana zargin wata mata mai suna Maryam Muhammad da laifin zuba wa mijinta da kishiyarta da yara biyu fetur, sannan ta banka musu wuta a unguwar Hotoro da ke cikin birnin Kano.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, kishiyar tata mai suna Firdausi Musa, mai shekaru 28 tare da ’ya’yanta ƙanana biyu sun samu munanan ƙonewa a sassan jikinsu.
Lamarin, wanda ya faru a daren jiya Litinin a yankin Mai Allo da ke Unguwar Hotoro, ya jefa mazauna yankin cikin firgici, yayin da ake tsare da wadda ake zargin a ofishin ’yan sanda na Mariri.
An bayyana sunayen yaran da suka jikkata da Khadija Ya’u mai shekaru 7 da kuma Isma’il Ya’u mai shekaru 3. Ana kula da lafiyarsu tare da mahaifiyarsu a Asibitin Ƙashi na Ƙasa da ke Dala da kuma Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano.
Mijinsu, Malam Saminu, wanda rahotanni suka ce shi ma ya samu ƙonewa yayin ƙoƙarin ceto su daga wutar, shi ma yana karɓar magani.
Da yake zantawa da jaridar Daily Trust, ƙanin Firdausi mai suna Buhari Musa Sa’ad, ya ce sun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3 na dare, cewa an banka wa ’yar uwarsa da mijinta da yaran biyu wuta daga kishiyarta.
A cewarsa, Firdausi ba ta yi ko makonni biyu ba da komawa gidan aurenta kafin wannan lamari ya faru.
“Firdausi tana da kusan shekaru 28. Yaran da suka ƙone kuwa su ne waɗanda ta zo da su daga aurenta na baya,” in ji shi.
Wata ’yar uwa ga Firdausi mai suna Rukayya ta kuma shaida wa Daily Trust cewa tun kafin harin, Firdausi ta yi ta ƙorafin cewa kishiyarta tana yi mata barazana da tsangwama.
“Mun kasance a kwance a nan, lokacin da aka kawo ta kuma ita da kanta ta gaya mana cewa kishiyarta ce ta zuba mata fetur sannan ta kunna ashana,” in ji ta.
Rukayya ta bayyana cewa tun da farko a ranar, Firdausi ta bar gidan saboda yawaitar barazanar da ake yi mata amma daga baya ta koma, bayan mijinta ya shiga tsakani.
Ƙoƙarin jin ta bakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano bai yi nasara ba kafin kammala haɗa wannan rahoto.
________












