Jihar Katsina Ta Samu Ministoci Biyu A Gwamnatin Tinubu


Allah Ya albarkaci Jihar Katsina da zaratan Ministoci har guda biyu a Gwamnatin Tarayya, bisa jagorancin Alhaji Bola Ahmad Tinubu.
A jerin sunaye 28 da Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya karanta, a matsayin sababbin ministocin da Shugaba Tinubu ya aika masu, akwai sunan Architrct Ahmad Dangiwa, daga Ƙaramar Hukumar Kankia da Barista Hannatu Musa Musawa, daga Ƙaramar Hukumar Musawa, duka daga Jihar Katsina.
Sauran mutanen sun haɗa da Abubakar Momoh, Amb Yusuf Maitama, Cheif Uche Nnachi, Dr. Beta Udoh, Dr. Doris anniche, Dave Umahi, Exenwa Wike da Muhammad Badaru Abubakar.
Akwai kuma Malam Nasir Ahmad Elrufai, Rt Hon Ebiribe Hon. Onyochuwecha, Hon. Oludimi Tunji Ojo,Hon Stella,Oju Kennedy, Bello Muhammad, Mr Dele Alake, Lateef Fabemi da Muhammad Idris.
Haka kuma akwai Elawale Edu, Waheed Adebayo, Mrs. Eman Sulaiman, Prof. Ali Pate, Prof. Joseph, Sen. Abubakar Kyari, Sen. John Enoh da kuma Sanata Sani Abubakar Danladi.













