Daga Auwalu Ɗanlarabawa
Wani magidanci ne bayan ya dawo gida daga wurin aiki, sai ya samu matarsa tana kuka, ga ‘yan uwanta suna taya ta haɗa kaya.
Cikin mamaki da kaɗuwa ya ce masu “lafiya?” Suka yi masa banza, ba su kula shi ba.
Bayan ya yi musu magiya, sai yayarta ta ce masa: “Ya za ka raina mana wayo, ka rubuto saƙon kar ta kwana, ka ce ka sake ta, ba ka son ka dawo ka gan ta a gidanka, kuma ka zo kana tambayar mu abin da ya faru?”
Shi kuwa sai ya rantse masu da cewa “wallahi tun safe aka sace wayata, ba ni na turo wannan saƙon ba.”
Ya karɓi wayar ƙanwarta ya kirawo wayar. Ya yi dace kuwa aka ɗauka. Ya ce, “Malam, wallahi ba sacen wayar da ka yi ne matsalata ba, amma laifin me matata ta yi ka sake ta?”
Ɓarawo ya ce, “tun da na sace wayar matarka take ta turo maka saƙo, tana cewa “Ka kira ni, ko ba za ka kira ba? Ina kuɗin cefane, ba ka bar mana abin da za mu ci ba… An koro yara daga makaranta, ka zo ka biya kuɗin makaranta… Me ya sa ba za ka ba ni amsa ba, wai da wa kake tare ne? Magana fa nake maka…”
Ɓarawo ya ci gaba da cewa: “Da na ga irin wahalar da kake ciki, ga musifar matarka, shi ne na sauƙaƙa maka ta hanyar sakar maka ita, ko ka huta.”
Tambaya:
Wai shin idan kai ne mijinta, wane mataki za ka ɗauka? Za ka jaddada sakin nata ko kuwa za ka haƙura da lalurarta, ka ci gaba da zaman aure da ita?













