UEFA 2025: WACE ƘUNGIYA CE ZA TA ƊAUKI KOFIN ZAKARU?
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Ya zuwa yanzu dai ƙungiyoyi huɗu ne suka fito matakin kusa da na ƙarshe, a Gasar Kofin Zakarun Nahiyar Turai ta bana. Waɗannan kuwa su ne, Paris Saint-Germain (PSG), Arsenal, Inter Milan da kuma Barcelona. A yayin da ƙungiyoyin za su kara a gobe (29) da jibi (30), shin wace ƙungiya ce a cikinsu za ta iya ɗaukar wannan mashahurin kofi a bana?
√ Paris Saint-Germain (PSG):
Kungiyar PSG tana ƙarƙashin jagorancin Luis Enrique kuma ƙungiya ce mai ƙarfi da haɗin kai. Duk kuwa da cewa fitaccen ɗan wasa Kylian Mbappé ya bar ta, sabbin ‘yan wasa kamar Vitinha, Neves, da Pacho sun ƙarfafa ƙungiyar sosai. A wasanninsu na baya-bayan nan, sun lallasa manyan ƙungiyoyi daga Ingila.
A nazari, ƙungiyar PSG tana da daidaito da ƙarfi a kowanne ɓangare. Salonsu na wasa mai burgewa da nuna ƙwarewa ne kuma sun yi dacen ƙwararrun ‘yan wasa. Hakan yana haska su a matakin farko da albishir cewa kofin bana zai iya kasancewa mallakinsu.
√ Arsenal:
A gasar bana, Arsenal ta ba da mamaki sosai ta hanyar fitar da babbar ƙungiya, Real Madrid, wacce take riƙe da kambin tarihin ƙungiyar da ta lashe kofin na Zakarun Turai har sau 15. A bana Arsenal ta yi wajerod da ita, ta lallasa ta da ci 5-1 a jimilla, wanda ya sa suka kai wasan kusa da na karshe karo na farko cikin shekaru 16.
Duk da samun rauni a Gasar Firimiya, ƙungiyar a ƙarƙashin jagorancin Mikel Arteta ta nuna juriya da fasaha a matakin Turai. ‘Yan wasa kamar Bukayo Saka da Gabriel Martinelli, suna taka rawar gani.
√ Inter Milan:
A bana, Inter Milan tana taka leda cikin tsari da tsaro sosai. Sun bari ƙwallo biyu kacal ta shiga ragarsu, a cikin wasanni 10, a gasar ta bana. Ɗan wasa Lautaro Martínez yana taka rawar gani sosai, inda ya zama ɗan wasan farko da ya ci ƙwallo a wasa 5 a jere a gasar ta bana. Tsarinsu da ƙwarewarsu sun sanya su cikin jerin manyan ƙungiyoyin da ke fafatawa a gasar ta bana, inda ake kallon za su iya lashe kofin.
√ Barcelona:
Barcelona mai gayya mai aiki, wacce take ƙarƙashin jagorancin Hansi Flick, ta canza zuwa salo mai sauri da kai farmaki sosai. Ƙungiyar ta ci gaba da lallasa manyan ƙungiyoyi kamar Real Madrid da Bayern Munich. Haziƙan ‘yan wasa kamar Lamine Yamal, Robert Lewandowski da Raphinha sun haɗa kai, sun kai farmaki da cin ƙwallaye sosai a kakar bana. Suna da ƙarfi a kai farmaki, amma ana iya samun ɗan rauni a ɓangaren tsaro.
Daga ƙarshe, cikin waɗannan zaratan ƙungiyoyi huɗu, kowacce na da damar da za ta ɗauki kofin nan, musamman idan suka jajirce amma dai an fi kallon ƙungiyoyin PSG da Bercelona da cewa cikinsu ɗaya za ta ɗau kofin nan.
Jama’a, mene ne ra’ayinku a kan waɗannan ƙungiyoyi huɗu kuma wacce kuke ganin za ta ɗauki kofin nan na bana? Ku bayyana a Comment Section.
______
👇













