Wasu Mutane Sun Kitsa Tayar Da Hargitsi A Najeriya – DSS
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Hukumar DSS ta bankaɗo wani mummunan shiri da wasu mutane suka kitsa da nufin haifar da mummunan hargitsi da tarzoma a sassan ƙasar nan da nufin shafa wa Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro baƙin jini, dangane da halin rayuwa da tattalin arzikin ƙasa suke ciki.
Kamar yadda Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar ta DSS, Peter Afunanya ya bayyana, a wata takardar manema labarai da ya fitar a yau Litinin, ya ce: “Bayanan tsaron sirri sun gano cewa, cikin waɗanda ke shirya wannan aika-aika, har da wasu ‘yan siyasa da ke hilatar shugabannin ɗalibai da na ƙungiyoyin ƙabilu, matasa da karkatattun ƙungiyoyi.”
Sai dai kuma hukumar ta ce tuni ta gano shugabannin masu kitsa wannan mugun aiki. Kuma tuni an saka komar bincike domin bibiyar su, domin daƙile aniyarsu ta jefa ƙasar nan cikin tashin hankali.
“Dangane da wannan al’amari, muna shawartar shugabannin jami’o’i da na manyan makarantu da su ja wa ɗalibansu kunne, domin su guji shiga harkar tayar da hargitsi. Haka ma iyayen yara su kula da ‘ya’yansu, su ƙaurace wa duk wani mutum da ke son jawo su cikin ayyukan karya doka da oda,” inji hukumar ta DSS.
Hukumar ta ce, a yayin da gwamnati ke ƙoƙarin magance wasu daga matsalolin da ke addabar ƙasar nan, tana gargaɗin duk wani mai son hargitsa zaman lafiyar al’umma da ya kiyaye. “Domin kuwa hukumarmu ba za ta ɓata lokaci ba wajen ɗaukar mataki mai girma a kansu.” Kamar yadda Afunanya ya bayyana.
~~~~~~~













