[contact-form][contact-field label=”Name” type=”name” required=”true” /][contact-field label=”Email” type=”email” required=”true” /][contact-field label=”Website” type=”url” /][contact-field label=”Message” type=”textarea” /][/contact-form]
RAYUWA
~~~~~~~
Ni Bashir Yahuza Malumfashi, na sadaukar da wannan waƙe ga ɗaukacin TALAKAWAN NAJERIYA, bisa halin matsi da jarabawa da ake ciki. Allah kawo sauƙi da sawaba – Amin!
~~~~~~~
Komai wuya ko akasi,
Kar ka yi kukan matsatsi,
Kar ka zamo mai taratsi;
Ka yi godiya ko ba hatsi,
Rabbi Allah bai mance ka ba.
~
Idan ka samu dami ɗaya,
Waiga ƙasa wani ba ɗaya,
Wani bai da ko da ‘yar tiya,
Sai dai ya je yai magiya.
Ƙarfin jiki ba ka kai shi ba.
~
Kai ne kake da ƙafa biyu,
Har ka ƙara da ido biyu,
Ga hannuwanka guda biyu,
Ka ɗauki saiti biyu-biyu.
Rahama ta Allah ba mutum ba.
~
Wani ko ƙafarsa guda ɗaya,
Wani ko idonsa guda ɗaya,
Wani babu hannu ko ɗaya,
Bai da tsaba ƙwaya ɗaya,
Iko na Allah ba na su o’o ba.
~
Wani ga gida tangameme,
Filin noma wangameme,
Dokin hawa sangameme,
Ga tulun ciki sunƙumeme,
Komai ya biɗa bai rasa ba.
~
Ga wata can kanta gashi,
Ya yi kwance ya yi laushi,
Kowa ya taɓa ya ji taushi,
Kowa ya gani zai murmushi,
Hikima ta Allah ba wanin ba.
~
Wata kanta sai yai kamar bal.
Babu gashi ƙwal yake tal.
Doguwa ce ga ta shantal,
Wata kau gajera ce ‘yar gajal.
Halittar Allah ba ta gaza ba.
~
Wani yai gabas wani yamma,
Wani dariya wani hamma,
Wani kasala wani himma,
Suturar wani ta yi tsumma.
Kowa da inda ya sa gaba.
~
Wani kam ɗan kasuwa ne,
Wancan kuwa ma’aikaci ne,
Shi ɗan uwa kafinta ne,
Ga wani nan injiniya ne,
Rayuwa ce ba ta zam ɗaya ba.
~
‘Yan uwana sai mu gane,
Rayuwa dai kar mu gune,
Godiyar Allah mu manne,
Komai ka gani ƙalubale ne,
Allah Yake yi ba mutum ba.
~
Ni Bashiru na gode Allah,
Ni ɗan Yahuza ba ni gilla,
Na Malumfashi ba ni illa,
Fasihin Galadima aƙalla.
Kariyar Allah ba mutum ba!
~~~~~~~
© Bashir Yahuza Malumfashi,
Talata 19-02-1445 (Hijiriyya),
05-09-2023 (Miladiyya).
~~~~~~~













