Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?
Daga Wakilinmu

__________
Kafar Sadarwar Intanet, Sahara Reportes ta ruwaito cewa an k@she shahararren mai sharhi kan al’amuran siyasa a kafafen sada zumunta, Ibrahim Khalil Ɗan Shagamu, a gidansa da ke Jihar Kano.
Ɗan Shagamu, wanda aka fi sani da laƙanin “Ɗan Shagamu International,” ya shahara ne ta hanyar sharhi da yake yi a fayafayen bidiyo kuma yake wallafawa a kafafen sada zumunta, ya shahara a da kuma sharhi kan harkokin siyasa, addini da al’amuran al’umma, musamman da suka shafi Jihar Kano da Arewa da ma ƙasa baki ɗaya.
Ƙungiyar Amnesty International Nigeria ta tabbatar da kis@n nasa a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X a yau Laraba, inda ta ce an gano gawarsa cikin jin! a gidansa da ke Kano.
Ƙungiyar ta ce: “Amnesty International ta yi Allah-wadai da kis@n mai sharhin siyasa a kafafen sada zumunta, Ibrahim Khalil Ɗan Shagamu, wanda aka gano g@warsa a yau cikin j!ni a gidansa da ke Kano.”
Ta ƙara da cewa: “An yank@ shi cikin mugun yanayi, bayan waɗanda suka k@she shi sun rinjaye shi.”
Har zuwa yanzu da aka haɗa rahoton nan, ba a samu cikakkun bayanai kan yanayin da ya kai ga kis@n nasa ba.
Rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta sun ce an k@she Ɗan Shagamu cikin mummunan yanayi, inda wasu suka bayyana yadda aka yi masa “yank@n rago,” wato y@nke maƙogwaro.
Amnesty International ta yi kira ga hukumomin Najeriya da su gudanar da cikakken bincike kan kis@n, tare da tabbatar da cewa an gurfanar da duk waɗanda ake zargi da hannu a lamarin a gaban ƙuliya, domin su fuskanci hukunci.
Ƙungiyar ta ce: “Dole ne hukumomin Najeriya su gudanar da bincike kan wannan lamari, tare da tabbatar da cewa an gurfanar da waɗanda ake zargi da alhakin kis@n a gaban shari’a.”
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta kuma bayyana damuwarta kan abin da ta kira, ƙara yawaitar barazana da tsoratarwa masu alaƙa da siyasa yayin da zaɓe ke ƙaratowa.
Amnesty ta ce: “Yayin da zaɓe ke ƙaratowa, muna ci gaba da samun rahotanni masu tayar da hankali kan barazanar kis@ da tsoratarwa da ke da alaƙa da siyasa.”
Labarin rasuwar Ɗan Shagamu ya jefa mabiyansa da mazauna yankin cikin jimami, inda da dama suka shiga kafafen sada zumunta domin bayyana kaɗuwarsu tare da yi masa addu’o’in neman rahama da gafara.
Abin tambaya a nan shi ne, shin wane ne ya k@she Ɗan Shagamu kuma laifin me ya aikata da ya cancanci ɗaukar r@nsa? Hukumomin tsaro ne kadai ke da alhakin binciko amsoshin wadannan tambayoyi.
__________













