• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, September 20, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Ta'aziyya

SANATA BELLO MANDIYA: Mun Yi Babban Rashi – Gwamnan Katsina

TA'AZIYYA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
September 9, 2026
in Ta'aziyya
0
SANATA BELLO MANDIYA: Mun Yi Babban Rashi – Gwamnan Katsina

Marigayi Sanata Bello Mandiya

17
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

SANATA BELLO MANDIYA: Mun Yi Babban Rashi – Gwamnan Katsina

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Malumfashi: Mun Yi Babban Rashin Uba

Malumfashi: Mun Yi Babban Rashin Uba

September 7, 2026
Inna Lillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal

Inna Lillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal

June 10, 2026

___________

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya nuna matuƙar kaɗuwa da alhini bisa rasuwar tsohon Sanatan da ya wakilci Katsina ta Kudu, Sanata Bello Mandiya, wanda ya rasu a Litinin da ta gabata, 7 ga Satumba, 2026, yana da shekaru 62 a duniya.

Gwamna Radda ya bayyana rasuwar Sanata Mandiya a matsayin babban rashi ga Jihar Katsina, musamman al’ummar Katsina ta Kudu da kuma ɓangaren siyasa.

“Na samu labarin rasuwar Sanata Bello Mandiya cikin matuƙar kaɗuwa da baƙin ciki. Rasuwarsa babban rashi ne ga Jihar Katsina da Najeriya,” in ji Gwamna Radda.

Ya bayyana marigayin a matsayin jajirtaccen ma’aikacin gwamnati wanda ya bayar da gudunmawa wajen ci gaban Jihar Katsina da Najeriya.

Marigayi Sanata Bello Mandiya

“Sanata Mandiya ya sadaukar da wani ɓangare na rayuwarsa wajen yi wa al’umma hidima, inda ya yi wa jama’armu aiki da kishin ƙasa da jajircewa. Gudunmawar da ya bayar za ta ci gaba da kasancewa abin tunawa,” in ji shi.

Gwamna Radda ya tuna cewa Sanata Mandiya ya taɓa riƙe muƙamin Shugaban Ma’aikatan Gwamna (Chief of Staff) a lokacin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari, kafin daga bisani aka zaɓe shi zuwa Majalisar Dattawa, inda ya wakilci Katsina ta Kudu daga shekarar 2019 zuwa 2023.

“Ƙwarewarsa da hidimar da ya gudanar a matakin jiha da tarayya, za su ci gaba da kasancewa wani ɓangare na tarihin rayuwarsa,” in ji Gwamnan.

Gwamna Radda ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayi Sanata Bello Mandiya da tsohon Gwamna Aminu Bello Masari da al’ummar Katsina ta Kudu da abokan aikinsa da abokan siyasa da ‘yan uwa da abokan arziki da kuma takwarorinsa na Majalisar Dattawan Najeriya ta 9.

“Ina roƙon Allah Maɗaukakin Sarki ya gafarta masa kurakuransa, ya saka masa da alherin ayyukan da ya aikata, ya kuma ba shi Aljannatul Firdausi. Allah ya bai wa iyalansa da waɗanda suke ƙaunarsa ƙarfin zuciyar jure wannan babban rashi mai raɗaɗi,” in ji Gwamna Radda.

__________

Previous Post

Gwamna Radda Zai Ƙarfafa Ayyukan Gidauniyar Zanna Tukur Tingilin

Next Post

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

Related Posts

Malumfashi: Mun Yi Babban Rashin Uba
Ta'aziyya

Malumfashi: Mun Yi Babban Rashin Uba

September 7, 2026
Inna Lillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal
Ta'aziyya

Inna Lillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal

June 10, 2026
Malumfashi An Yi Babban Rashi
Ta'aziyya

Malumfashi An Yi Babban Rashi

May 11, 2026
Next Post
Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

General Buratai (A Poem)

General Buratai (A Poem)

April 26, 2026
Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

July 8, 2023
SAƘON JUMU’A: Daga Malam Anas Saminu Ja’en

SAƘON JUMU’A: Daga Malam Anas Saminu Ja’en

October 6, 2023
BATUN WATAN SALLAH A NAJERIYA

BATUN WATAN SALLAH A NAJERIYA

April 8, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso
  • JAGORA: Leader of the Masses
  • MALAM SULE LAMIDO: Jagoran Talakawa Ya Cika Shekaru 78

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

September 20, 2026
JAGORA: Leader of the Masses

JAGORA: Leader of the Masses

September 17, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.