Oh ni Shanshani! Ina tsakar yawona sai na tsilga Gidan Dutse, inda mulaka’un Najeriya ke sha’aninsu.
Tun daga nesa na jiwo rurin kalangu, wani mawaƙi yana ta zuba waƙa da yaren unbatunbatun. Jin haka kunnuwana suka sake buɗewa kamar na giwa, idanuwana suka ƙara bullowa kamar na autan ƙururu.
Ina dubawa, sai na ga sabon angon Najeriya da matarsa suna ta tiƙar rawa, ana ta yi masu taɓi. A gefe guda kuma na ga mataimakinsa shi ma yana tasa rausayar, tare da mai ɗakinsa. Rawa suke riris kamar ba gobe.
Ni kuwa na nisa, na kalli wani daga cikin ‘yan kallo, na ce wai mene ne dalilin wannan shagali haka, inda mulaka’u suke shagala da sharholiya haka?
Nan take, ya kalle ni galala cikin mamaki, ya ce mani: “Haba Shanshani, hala ba ka da labarin ɗazu-ɗazun nan aka rantsar da su kama ragamar mulkin uwar Afrika – Najeriya?”

“Ni kuwa ke da labari,” na sanar da shi, sannan na ci gaba da cewa: “Ai bai kamata su ɓige da casu ba, musamman idan aka yi la’akari da matsanancin yanayin da ayyuhannasu ke ciki.
“Shin ba su san cewa wannan lokaci ne na jajircewa da aiki wurjanjan ba? Ba su san cewa lokaci ne da ya kamata su ɗaura ɗamarar ceto talaka daga ƙangi ba?
“Lallai wannan ba Lokacin sharholiya ba ne ga shugabanni. Idan suka sake, kamar yanzu ne lokaci zai ƙure masu, lokacin zaɓe zai zo.”
Mutumin nan ya kalle ni, kallo na amincewa da dukkan abin da na faɗa. “Babu shakka wannan ba lokacin shagala ba ne…” in ji shi.













