KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Daga Mukhtar Mudi Sipikin
~~~~~~~
A yau SHANSHANI ya kamu da mura, dalili ke nan ya makara, bai kai ziyara gidan Malam Na Fagge ba da wuri. Don haka koda ya isa, ba tare da ɓata lokaci ba aka miƙo masa ambulon mai ɗauke da Shaguɓen KAMUN LUDAYIN JEMAGE na wannan makon. Ga abin da yake cewa:
~~~~~~~
Kurciya ta yi tagumi ta yi jugum tana tunani. Ga ƙwalla na zuba. Kowa ya kalle ta ya san tana cikin mayuwacin hali.
Tattabara cikin damuwa ta ce: “Kurciya lafiya dai? Irin wannan tagumi haka har da ƙwalla; wani abu ne ya faru?”
Kurciya ta ja dogon numfashi game da ajiyar zuciya sannan ta amsa da cewa: “Ƴar uwa meye ma bai faru ba? Kullum shugabannin Dajin nan cikin ƙoƙarin jefa mu wani hali suke da sunan gyara. Ɗazu na je sheƙar Duba Lafiya, abin da na gani ya ba ni tsoro. Na ga marasa lafiya birjik amma ba mai duba su. Wai Tsuntsaye masu duba lafiya ne suka tafi yajin aiki.”
Bainu wadda ke can gefe amma tana jiyo abin da su Kurciya ke cewa, ta kada baki ta ce: “Kawuna jiya ya cika saboda ba mai duba shi. Allah Ya ji ƙan shi.”
Sauran tsuntsaye suka amsa da “Amin!”
Waje ya yi tsit, can Gado ya ɗaga murya ya ce: “Zaman nan fa da sake, kullum ƙara takure ƙananan Ttsuntsaye ake. Na ji labarin wai za a ƙara kuɗin sinadarin makamashin zirga-zirga, ga farashin tsaki kullum hauhauwa yake; har ta kai tsuntsaye yanzu yin ƙoto sau biyu a yini sai mai tsananin rabo.”
Kanari ta ce: “Ni ba abin da ya daɗe yana mun raɗaɗi a zuciya irin maganar da Shugaban Majalisar Ragon-Maza ya yi, har ya bayyana a majigi yana ce wa ‘yan uwansa su kwantar da hankalinsu, an tanadar musu sulalla masu ɗimbin yawa don su more hutun da za su tafi. Wato dai mu an ɗauke mu bayi ke nan ko?”
Hazbiya ta numfasa ta ce: “Ga kuma yaƙi da ake ta ƙoƙarin sai an assasa tsakaninmu da ‘yan uwanmu kuma maƙwabtanmu. Muna cikin wannan ƙangin za a ƙaro mana wata musibar. Kaico!”
Cakwaikwaiwa ta ce: “Jemage ke nan ake faɗa muku! Shi ai kullum sama yake hangowa, ba ruwansa da lura da halin da na ƙasa ke ciki. Na ji an cire sunayen tsuntsaye uku, ciki har da Yautai, wanda aka tura Majalisar Ragon-Maza don a tantance su ko?”
Bainu ta amsa da cewa : “Eh, an ce wai bai iya bakinsa ba. Allah Ya kyauta. Ita kuma ‘yar uwarmu dangin Agwagwa, Ungulu ce ta ba da umarnin a sauya ta.”
Da yake dare ya tsalla, Tsuntsaye suka buƙaci Alhudahuda ya yi addu’a ga tsuntsayen da iccen sheƙar ibada ya yi sanadiyyar su tafiya gidan gaskiya. Ai ko ya ja addu’a, aka shafa, aka yi sallama.
~~~~~~~
Malam Mukhtar Mudi Sipikin, marubuci, sha’iri, ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa; ya rubuta wannan shaguɓe a ranar 12-08-2023.
~~~~~~~













