• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, September 20, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Shugaba Tinubu, Manyan Sojoji, Mutallab, Mangal, Sarki Sanusi II Za Su Halarci Ƙaddamar Da Littafin Janar Buratai

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
September 10, 2026
in Adabi
0
Shugaba Tinubu, Manyan Sojoji, Mutallab, Mangal, Sarki Sanusi II Za Su Halarci Ƙaddamar Da Littafin Janar Buratai

Shugaba Tinubu, Alhaji Ɗahiru Mangal, Alhaji Umaru Mutallab da Sarki Muhammadu Sanusi ll

31
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Shugaba Tinubu, Manyan Sojoji, Mutallab, Mangal, Sarki Sanusi II Za Su Halarci Ƙaddamar Da Littafin Janar Buratai

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

ALLAH TSIN€ WA MAƘIYA MANZO (SAW)

ALLAH TSIN€ WA MAƘIYA MANZO (SAW)

September 12, 2026
Alhaji Sule Lamido: Jagoran Talakawa Na Haƙiƙa

Alhaji Sule Lamido: Jagoran Talakawa Na Haƙiƙa

August 29, 2026
Shugaba Tinubu, Alhaji Ɗahiru Mangal, Alhaji Umaru Mutallab da Sarki Muhammadu Sanusi ll


__________
Ana sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Manyan Hafsoshin Sojojin Najeriya za su halarci bikin ƙaddamar da wani sabon littafi da ya yi nazari kan shugabanci, sauye-sauye da kuma sauya fasalin Rundunar Sojin Najeriya a ƙarƙashin tsohon Shugaban Rundunar Sojoji, Laftanar Janar Tukur Yusufu Buratai (mai ritaya).

Littafin mai taken “Military Transformational Leadership in Action: The Buratai Era,” wanda Dakta M. S. Abubakar ya rubuta, za a gabatar da shi ga jama’a a ranar Laraba, 16 ga Satumba, 2026, a Zauren Taro na Rundunar Sojojin Najeriya da ke Asokoro, Abuja.

A cewar wata sanarwa da Shugaban Kwamitin Shirye-shiryen taron, Dakta Ahmad Manzo, da Babban Daraktan Kamfanin Clarivox Creative Limited, Mista Segun Adeyemi, suka fitar a jiya Laraba, za a fara taron da ƙarfe 9:45 na safe.

An sanya Shugaban Ƙasa Tinubu a matsayin Babban Bako na Musamman, yayin da ake sa ran tsohon Ministan Tsaro, Alhaji Umaru Abdul Mutallab, zai jagoranci taron.

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ne zai gabatar da littafin, yayin da Shugaban Kamfanin Max Air, Alhaji Dahiru Barau Mangal, zai kasance ɗaya daga cikin manyan masu ƙaddamar da littafin. Ana kuma sa ran Manjo Janar I. D. Penap (mai ritaya) zai yi bitar littafin.
Masu shirya taron sun ce ana sa ran dukkan Hafsoshin Rundunonin Sojoji, ciki har da Shugaban Rundunar Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, za su halarci taron a matsayin manyan baƙi na musamman.

Littafin ya yi nazari kan shekarun da Buratai ya yi a matsayin Shugaban Rundunar Sojoji, inda aka fi mayar da hankali kan matakan shugabanci, sauye-sauyen hukumomi da kuma ƙalubalen tsaro da Rundunar Sojojin Najeriya ta fuskanta a wannan lokaci, musamman yaƙin da aka yi da masu tayar da ƙayar baya da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.

A cewar Abubakar, littafin bai tsaya kawai wajen rubuta tarihin wa’adin wani kwamandan soja guda ɗaya ba, sai dai ya yi nazari kan alaƙar da ke tsakanin shugabanci, sauya fasalin hukumomi da kuma tsaron ƙasa.

Ya ce, “Babban manufar wannan littafi ita ce yin nazari kan shugabanci a aikace, wato yadda aka tsara matakai, aka aiwatar da sauye-sauye da kuma yadda hukumomi suka mayar da martani bisa haƙiƙanin ƙalubalen da Rundunar Sojojin Najeriya ta fuskanta a wani lokaci mai matuƙar wahala a tarihin tsaron ƙasar.”

Ya ce wasu daga cikin manyan tsokacin da littafin ya kawo, sun haɗa da yadda rundunonin sojoji suke tinkarar barazanar tsaro da ke sauyawa da kuma rawar da shugabanci ke takawa wajen daidaita hukumomi da sababbin yanayi.

Ana sa ran bikin gabatar da littafin zai samu halartar manyan jami’an gwamnati, hafsoshin soja masu aiki da waɗanda suka yi ritaya, sarakunan gargajiya, jami’an diflomasiyya, malamai da masu bincike da sauran masu ruwa da tsaki.

Daga cikin sarakunan gargajiya da ake sa ran za su halarta, akwai Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, da Olowu na Kuta, Oba Hameed Oyelude Makama Tegbosun III.

Shirin taron zai kuma ƙunshi tattaunawar ƙwararru wadda Amina-Akano Bello da Manjo Janar Victor Ezegwu (mai ritaya) da Rear Admiral Adamu Biu (mai ritaya) da Farfesa Phillip Dahida za su gabatar. Haka kuma marubucin littafin, Abubakar, zai kasance a cikin masu tattaunawar.

Abubakar ya ce an rubuta littafin ne domin adana ƙwarewa da abubuwan da hukumomi suka gabatar a baya, tare da ƙarfafa yin tunani mai zurfi kan tsarin tsaron Najeriya.

Ya ce, “Hukumomin tsaro suna ci gaba da samun sauye-sauye ne ta hanyar yin nazari kan abubuwan da suka fuskanta, tsarin da ya yi aiki da wanda bai yi ba da tsarin ya sauya da kuma darussan da ya kamata a ci gaba da riƙewa.”

Adeyemi, wanda ya haɗa gwiwa tare da Dakta Manzo wajen bayar da sanarwar, ya ce rubuta muhimman lokuta a tarihin hukumomin Najeriya, na iya samar da tushe mai kyau wajen koyo da kuma gudanar da muhawara mai ma’ana.

Ya ce littafin zai ba ƙwararrun sojoji, masu bincike, masu tsara manufofi da sauran jama’a damar yin nazari kan wani muhimmin lokaci a tarihin tsaron ƙasar, tare da duba darussan da za a iya amfani da su wajen tsara makomar ƙasar.
__________

Previous Post

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

Next Post

MALAM DIKKO

Related Posts

ALLAH TSIN€ WA MAƘIYA MANZO (SAW)
Adabi

ALLAH TSIN€ WA MAƘIYA MANZO (SAW)

September 12, 2026
Alhaji Sule Lamido: Jagoran Talakawa Na Haƙiƙa
Adabi

Alhaji Sule Lamido: Jagoran Talakawa Na Haƙiƙa

August 29, 2026
ALBARKAR HAUSA
Adabi

ALBARKAR HAUSA

August 26, 2026
Next Post
MALAM DIKKO

MALAM DIKKO

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

June 17, 2026
Za Mu Inganta Rayuwa Da Ayyukan ‘Yan Jarida – Minista Idris

Za Mu Inganta Rayuwa Da Ayyukan ‘Yan Jarida – Minista Idris

October 18, 2023
COMMENDATION: Essence of Loyalty to a Principal

Muhimmanci Da Tasirin Biyayya Ga Ubangida

August 25, 2025
Abin Da Ya Sa Muka Karrama Jami’an Tsaro A Malumfashi

Abin Da Ya Sa Muka Karrama Jami’an Tsaro A Malumfashi

October 5, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso
  • JAGORA: Leader of the Masses
  • MALAM SULE LAMIDO: Jagoran Talakawa Ya Cika Shekaru 78

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

September 20, 2026
JAGORA: Leader of the Masses

JAGORA: Leader of the Masses

September 17, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.