Tsakanin Rarara Da Pantami: Yayin Da Maroƙi Ya Zaci Shi Wani Ƙusa Ne…
Daga Mohammed Bello Doka
__________
Lokacin da Davido ya kira Rarara da jahili, a yayin musayar kalamai da suka yi kan sace ɗaliban makaranta a Jihar Oyo, masu kare Rarara sun gaggauta lulluɓe shi da rigar tausayi. “Rarara Musulmi ne,” suka ce. “Rarara ya yi karatun tsangaya,” suka tunatar da jama’a. “Rarara fitaccen mawaƙin Arewa ne da ake girmamawa, don haka bai kamata a kwatanta shi da wani Kiristan Kudancin kamar Davido ba.” Duk wata suka da ake yi wa Rarara, a cewarsu, hari ne kan Musulunci da kuma martabar Arewacin Najeriya.
Sai kuma Rarara ya zauna a gaban kyamara ya yi wa Sheikh Isa Ali Pantami kalamai na cin mutunci waɗanda ba su dace a maimaita su ba.
Mutumin da aka kare da hujjar addini, shi ne yanzu ya tauye martabar addinin da aka jingina wajen kare shi. Muryoyin da suka yi ihu suna zargin Davido da ƙyamar Musulunci, yanzu sun yi shiru yayin da Rarara ke jefa munanan kalamai ga ɗaya daga cikin manyan malamai da ake girmamawa a Arewacin Najeriya. Farfesa ne. Tsohon Minista ne. Mutumin da ya shafe shekaru masu yawa yana hidimar ilimi har ya samu matsayi na musamman a zukatan miliyoyin mutane.
Rarara kamar filfilo ne da ya ɗauka shi tsuntsu ne; maroƙin da yake jiji da kansa, yana tunanin shi wani ƙusa ne a ƙasa. Kuma idan irin wannan ruɗin ya kama mutum, lokacin taɓarɓarewa da faɗuwarsa ce take zuwa, kodayake ba a san yaushe ne ƙarshen nasa zai zo ba.
A al’adar Hausawa, bambanci tsakanin malami da maroƙi ba bambancin sana’a kaɗai ba ne. Bambanci ne mai tushe. Malami yana samun matsayinsa ne ta hanyar ilimi, taƙawa da hidimar al’umma. Darajarsa tana ginuwa ne a kan shekaru na koyo da koyarwa da kuma shiryar da al’umma zuwa ga kyawawan ɗabi’u. Maroki kuwa, a gefe guda, mai nishaɗantarwa ne, wanda sana’arsa ita ce yabon masu mulki kuma rayuwarsa tana dogara ne da kyautar masu iko.
A ma’anarta ta tarihi, maroƙi mai bara ne. Ba a matsayin zagi ba, amma a matsayin ma’ana. Ba ya rera waƙa domin gaskiya, sai domin abin da zai samu. Muryarsa ba tasa ba ce gaba ɗaya.
Wannan bambanci ya daɗe yana tabbatar da daidaiton al’ummar Arewa tsawon zamani. Malamai sun gina iyalai da al’umma, sun koyar da tawali’u, ladabi, ɗa’a da tsoron Allah. Tasirinsu ya samo asali ne daga ilimi da kyawawan halaye, ba daga tafi ko kusanci da masu mulki ba. Saboda haka babban take haƙƙi ne, idan maroƙi ya kuskura ya zagi malami. Suka wani abu ne, rashin girmamawa kuma wani abu ne daban. Lokacin da Rarara ya tunkari Sheikh Pantami da shaguɓe, ba wai yana sukar wani fitaccen mutum ba ne kawai; yana ɓatanci ne ga cibiyar ilimin Musulunci da masu kare shi suka ce shi ma yana wakilta.
Sheikh Pantami yana da daraja ba saboda wani muƙamin siyasa da ya taɓa riƙewa ba, sai saboda shekaru masu yawa da ya sadaukar wajen ilimin Musulunci, koyarwa da gudunmowar ilimi. Tasirinsa ya wuce siyasa. Matsayinsa ya samo asali ne daga ilimi da ɗabi’a, ba daga tafi ko kusanci da iko ba. Wannan girmamawa ba za a iya rushe ta saboda waƙa ko saɓanin siyasa kawai ba. Lokacin da Rarara ya zagi Sheikh Pantami, ya zagi duk Musulmin da ke kallon malamai a matsayin jagororin ɗabi’a. Ya zagi kowane ɗalibin da ya zauna a gaban malamai yana neman ilimi. Ya kuma zagi kowane iyali da ya taɓa neman shawarar malamai a lokacin ƙunci.
Ka yi la’akari da wannan abin mamaki. Mahaifiyar Rarara ma ta taɓa faɗawa hannun ‘yan bindiga. Ya biya kuɗin fansa. Bai yi wata magana kan gwamnati ba. Ya yi shiru yayin da iyalinsa ke cikin wahala. Amma lokacin da Davido ya yi magana kan yaran makaranta da aka sace daga birnin Los Angeles, Rarara ya fusata ƙwarai. Ya kira fitaccen mawaƙin da ɗan ta’adda. Ya zarge shi da tona asiri. Ya yi alfahari da kusancinsa da Shugaba Tinubu.
Mutumin da bai iya kare mahaifiyarsa ba ya tsaya yana biya wa fitaccen tauraron duniya darasi kan tsaro. Mutumin da fadar mulki ke mallakar muryarsa, ya kai hari ga mutumin da ya yi magana cikin ‘yanci. Arewa ce ta fi shan wahalar rashin tsaro. Hankalin duniya kan matsalar sace mutane a Najeriya zai iya zama alheri. Amma Rarara ya ga hakan a matsayin barazana, ba ga mutanensa ba, sai ga masu ɗaukar nauyinsa.
Rayuwar Rarara ita kanta tana nuna labarin mutumin da ke ƙoƙarin samun matsayin da bai cancanta ba. Iƙirarinsa na samun digirin girmamawa daga wata jami’a ya gamu da ƙaryatawa daga ita kanta cibiyar da aka ce ta ba shi, abin da ya bayyana cewa lamarin ya kasance na yaudara. Ga wani mutum mai matsananciyar neman karɓuwa, amma daga ƙarshe ya gamu da abin kunya. Wannan hoto ne mai cike da takaici na maroƙin da ke neman rawanin da ba a tanadar masa ba.
Ko addininsa ma ba zai iya kare shi ba. A wasu tsauraran fahimtocin fiƙihun Musulunci, kiɗa da bara, ana kallonsu a matsayin haram. Mutumin da ke iƙirarin zurfin sanin Alƙur’ani amma ya gina rayuwarsa gaba ɗaya kan waƙoƙin yabo da dogaro da siyasa, yana rayuwa cikin saɓo. Ya kai hari ga malamin da hidimarsa ga Musulunci ta shafe rayuwa baki ɗaya, alhali shahararsa tasa ta ɗan lokaci ce. Yana alfahari da sanin sirrika, amma bai iya kare mahaifiyarsa ba. Yana kiran wasu ‘yan ta’adda, alhali yankinsa na ci gaba da zubar da jini.
Rarara ya ruɗu da siyasa a matsayi na dindindin. Ya ɗauki kusanci da iko a matsayin iko kansa. Ya manta cewa fadar da ke ciyar da shi a yau, tana iya watsar da shi gobe. Shahara ta ɗan lokaci ce. Daraja kuwa ana samunta ne bayan rayuwa mai cike da hidima. Lokacin da fitattun masu sana’ar samar da nishaɗi suka yi watsi da al’adu da ƙa’idojin addini da suka daɗe suna riƙe al’umma, suna aika wa matasa saƙo mai haɗari game da yadda ya kamata a riƙa mu’amala da manya, malamai da masu ilimi, lamarin ba zai haifar da ɗa mai ido ba.
Arewacin Najeriya ya daɗe yana ware wa malamansa matsayi na musamman. Bambancin ra’ayi abu ne da ba makawa. Amma bai kamata ya rikiɗe zuwa izgili ko cin mutuncin waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen neman ilimi da shiryar da al’umma ba. Rarara yanzu ya aikata babban kuskure a sana’arsa. Ya juya wa ginshiƙan da suka ɗora al’ummarsa baya. Ya zagi malami. Ya kare gwamnatin da ta gaza kare mahaifiyarsa. Kuma da hakan, ya bayyana kansa a matsayin abin da yake a zahiri: maroƙin da ya ruɗu da ɗan abin da ya samu na wucin gadi a matsayin ɗaukaka.
Waɗanda suka lulluɓe shi da rigar Musulunci domin kare shi daga Davido, yanzu dole su fuskanci gaskiya. Mutumin da suka kare, shi ne yanzu ya ci mutuncin ilimin Musulunci kansa. Asalin Musuluncin da suka ɗaga tutarsa wajen kare shi, shi ne yanzu ya tauye martabarsa. Ba za su iya riƙe bangarorin biyu lokaci guda ba. Idan za a kare Rarara saboda shi Musulmi ne, to dole kuma a hukunta shi a matsayin Musulmi saboda zagin ɗaya daga cikin manyan malaman Musulunci da ake girmamawa.
Lokacin da maroƙi ya ruɗu da amfanin da ake da shi na ɗan lokaci a matsayi na dindindin, lokacin da mai bara ya ɗauka shi wani jan wuya ne, rushewar ɗaukakarsa tabbas ce. Ƙasa ma ta riga ta fara zamewa daga ƙarƙashin ƙafafunsa. Ruwa a cokali dai, ya ishi mai hankali wanka!
_________
Mohammed Bello Doka
E-mail: bellodoka82@gmail.com












