Maryam ‘Yar Aljanna
__________
Gabatarwa:
Wannan labari ƙirƙirarre ne kuma mun same shi ne daga haziƙin adibi, Malam Nasiru G. Ahmad. Labari ne mai mai cike da abin tausayi da kuma darussa masu yawa.
__________

Wani mutum ne da matarsa mai suna Maryam, suna zaman lafiya da kyautata wa juna. Rannan sai wata tafiya ta kama shi, ta fuskar neman abincinsa. Ya shiga tunanin wanda zai bar wa wasicin kula da ɗawainiyar matar ta yisa saboda tana da tsananin kyau, irin na a tsegunta wa yarima.
Bai samu wanda zai ɗora wa wannan nauyi ba da ya wuce ɗan uwansa shaƙiƙi. Don haka ya danƙa al’amarin kula da iyalin nasa a hannunsa, ya kama hanya ya tafi.
Mutumin bai daɗe da tafiya ba, sai Shaiɗan ya shiga ya fita a zuciyar ɗan uwan nan da aka bar wa wasici, har ya je ga Maryam, matar ɗan uwan nasa da nufin neman ta. Ita kuwa ta ƙeƙasa ƙasa ta ce ba ta san wannan mugun aiki ba. Ya yi mata barazanar cewa, idan ba ta yarda ba zai kunyata ta. Ita ko ta ce ya yi duk abin da ya so, ita kam ba za ta ci amanar mijinta ba. Allah kuma zai kare ta daga kaidinsa.
Bayan dawowar maigidan, sai ɗan uwan nasa ya shaida masa cewa matarsa ta yi ta ƙoƙarin sa shi ya neme ta amma ya ƙi. Ba tare da wani kokwanto ba mijin matar nan ya sake ta, ya kuma kore ta daga gidansa. Ga shi ita Maryam ba ‘yar wannan garin ba ce. Mijin nata ya hana ta ko ɗan kuɗin da za ta yi guzuri da shi.
Maryam ta fita ba ta san inda ta nufa ba, har Allah ya kai ta can bayan gari, gidan wani mutum mai ibada kuma ma’abocin zuhudu. Ya tambaye ta labarinta, ta faɗa masa. Ya nemi ta zauna ta riƙa yi masa rainon wani ƙaramin yaronsa bisa wani lada da ya yanka mata. Ta kuwa amince, ta zauna a gidan wannan mai ibada.
Ana nan sai mai ibadar nan ya yi wata ‘yar tafiya. Sai hadiminsa ya shiga wajen Maryam, ya neme ta da ta biya masa buƙatarsa. Ita kuwa ta ce atafau ba dai ita ba. Ya ce in ba ta yarda ba, zai ƙulla mata sharri. Ta ce ya yi duk abin da ya so, Allah zai fisshe ta sharrinsa.
Sai hadimin ya sami yaron da take raino ya kashe shi.Yayin da mai ibada ya dawo, sai hadimin nan ya ce matar nan ce ta kashe yaron. Mai ibada ya yi matuƙar baƙin ciki da jin haka, ya fusata ainun. Amma sai ya tuna da faɗin ubangiji da ya ce, “Da masu haɗiye baƙin ciki, da masu yin afuwa ga mutane (da suka saɓa musu). Allah kuma yana son masu kyautatawa.” (Aal-Imran: 134) Sai ya haɗiye baƙin cikin nasa, ya ce ya yafe mata. Ya kuma kawo ladan aikinta na kwanakin da ta yi ya ba ta, ya nemi ta bar masa gidansa.
Cikin jimami da alhini, Maryam ta fita daga gidan Malam mai Zuhudu. Da yake ba ta san inda za ta nufa ba, sai ta yi nufin komawa cikin gari. Tana isa ƙofar gari sai ta iske wasu mutane sun kama wani mutum, suna ta dukan sa. Ta tsaya ta tambayi me ya yi? Sai suka ce mata bashin wasu kuɗi ake bin sa. Muddin kuwa bai biya ba, to ya zama bawan masu bin sa bashin.
•••
• A saurari kashi na biyu na wannan labari.
__________












