Marubutan Hausa sun kafa gidauniya domin tallafa wa iyalan marigayi Auwal Garba Ɗanbarno, wanda Allah Ya amshi ransa a kwanakin baya, a sanadiyyar haɗarin mota.
A saƙon marubutan, suna cewa:
“Haƙiƙa ba gatan da za mu yi masa da tabbatar da muna ƙaunar sa sai ta addu’a da ƙoƙarin haɗa kwabo da ɗari don tallafa wa iyalinsa da mahaifansa da ya bari.
“An tattauna sosai kuma an tsayar da shawarar a yi ƙoƙarin yin gidauniyar da za a tallafa wa marayunsa da ya bari don hidimar yau da gobe. An kafa kwamiti a cikin marubuta da makusantansa, an kuma aminta da in aka tara abin da aka samu za a yi amfani da shi gun tallafin karatun ƙananan yara goma day a bari. Idan kuma an samu isassun kuɗi, a ba matansa jari don fara sana’ar gida don rage wahalar ciyarwa da sauran lalurori.
“Allah ya karɓi ransa a lokacin da duk nauyin mahaifansa, uwa da uba da na matansa biyu da yaransa goma, har na marayu biyar da yake riƙo.
“Muna roƙon don Allah bayin Allah ku taimaka komai kanƙantarsa, daga mai ɗari har miliyan, komai Allah Ya hore, don nuna masa ƙauna da jin daɗin halayensa na alheri da kowa ya shaida. Don Allah bayin Allah a taimaka.
“Ga mai son taimako don Allah a saka a asusun banki kamar haka:
Account Name: Rahma Abdulmajid Sherif.
Account Number: 2080944326.
Bank: United Bank For Africa (UBA).
Allah Ya ba da ikon taimakawa, alfarmar Annabi Muhammadu (saw).
Allah Ya ji ƙan waɗanda suka riga mu gidan gaskiya, Ya dauwamar da su a Aljanna firdausi. Allah kuma Ya saka wa waɗanda suka taimaka Ya sa ya zame musu silar ɗaukaka da buɗi.












