Wa Ke Tsoron Malam Elrufa’i Ya Zama Minista?
Malam SHANSHANI, wai shin don Allah wane ne ke jin tsoron ganin Malam Nasiru Elrufa’i ya zama Minista a Gwamnatin Tinubu?
Wannan tambaya ce wani ya yi inda ni kuma ba tare da ɓata lokaci ba, na shiga nazari, na tanadar masa da waɗannan bayanan a matsayin amsa:
Na farko dai, manyan waɗanda ke tsoron ya zama Minista, su ne Manyan Dillalan Makamashi, waɗanda suka haɗa har da wasu attajirai da ke mallakar kamfanonin raba wutar lantarki a Najeriya.
Babban abin da waɗannan mutane suke tsoro shi ne, suna da kyakkyawan zaton za a ba shi Ma’aikatar Makamashi ne. Kuma suna sane da irin himmarsa da jajircewarsa a duk inda ya samu kansa. Don haka idan ya zama Minista a wannan ma’aikata, zai kawo masu cikas. Zai tabbatar da cewa an yi duk abin da ya dace wajen daƙile cuwacuwar da ake yi a samar da lantarki a ƙasar nan. Zai tabbatar da cewa lallai duk wani mai kawo matsala a wadata lantarki a ƙasar nan, an yi maganinsa. Wannan shi ne dalilin tsoron nasu kuna dalili ke nan suke ta haƙilon ganin Majalisar Dattijai ba ta wanke shi ba
Rukuni na biyu da suke adawa da Malam Elrufa’i, su ne wasu ‘yan siyasa da suke ganin zai hana su rawar gaban hantsi a Gwamnatin Tinubu, musamman ma suna ganin yana da tasiri a wasu jihohin Arewa.
A kan haka, wasu ‘yan siyasa a Jihohin Kaduna da Kano, ba su son ganin Malam Elrufa’i ya zama Minista. Misali a Kano, an san cewa yana da alaka da fahimta tsakaninsa da Gwamna Abba Kabir Yusuf. Haka kuma an san irin zumunci da amanar da ke tsakaninsa da Sarkin Kano (murabus), Malam Muhammadu Sanusi II.
Waɗannan mutane suna tsoron idan Elrufa’i ya zama Minista, komai na iya faruwa a siyasance a Kano. Kuma suna tsoron zai iya taka rawa wajen ganin an mayar da aminin nasa a gadon Sarautar Kano.
Wasu mutane kuma da suke adawa da Malam Elrufa’i, su ne ‘yan Shi’a, waɗanda suke ƙullace da shi saboda rawar da ya taka wajen korar Malam Elzakzaky daga Zaria.
‘Yan Shi’a ba za su riƙe hannu su ga Malam Nasiru ya samu nasarar zama Minista ba. Dalili ke nan ma lokacin da aka ambata sunansa, suka shirya zanga-zangar nuna rashin amincewa da shi, suka je har kofar Majalisar Tarayya, ɗauke da kwalayen da ke ɗauke da rubuce-rubucen adawa.
Wasu kuma da ke adawa da Malam Elrufa’i kuma suke tsoron ganin ya zama Minista, su ne wasu “cabal” na tsohuwar Gwamnatin Muhammadu Buhari.
Irin waɗannan mutanen, suna tsoron kada Elrufa’i ya zama Minista, domin zai iya rikita masu lissafinsu na siyasa, musamman a Arewa, a zaɓe na gaba.
Ana zargin cewa, irin waɗannan rukunnan mutane ne suke ta haƙilo da faɗi-tashi, suke bin hanyoyin daƙile aniyar Malam Nasiru ta zama Minista. Su ne suke bin kwanoni a Majalisar Tarayya, suke ɗaukar nauyin rubuce-rubucen ɓatanci a kafafen watsa labarai, domin cin ma manufarsu.
Abin jira a gani shi ne, shin za su yi nasara? Shin Shugaba Tinubu zai jefar da Elrufa’i haka, duk da cewa shi ba ƙashin yadawa ba ne? Kowa dai ya san irin gwagwarmayar da ya sha wajen ganin Shugaba Tinubu ya yi nasara.













