Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

_______________
Hukumomin sabon Gidan Rediyon Afrika (Radio International – ARI), wanda zai fara gabatar da shirye-shiryensa a gobe Juma’a, ya naɗa shahararren ɗan jarida, Hassan Maina Kaina a matsayin Babban Edita kuma Shugaban Hukumar Gudanarwa (Editor-In-Chief/CEO).
Haka kuma, Hukumar gudanarwar, a wata takardar manema labarai da ta saki, ta sanar da sunayen shugabannin da za su jagoranci tashar rediyon, wacce aka kafa domin ƙarfafa muryoyin ‘yan Afrika da kuma gina labaran gaskiya na nahiyar.
Bayan Hassan, wanda aka naɗa a muƙamin Babban Edita kuma Shugaban Hukumar Gudanarwa, an kuma naɗa Mohammed Abba Jami’in Tsara Shirye-shirye da Tabbatar da Gudanuwar Ayyuka (Planner/Fixer). A’isha Mu’azu, ita ce Mataimakiyar Edita, wacce za ta jagoranci ɓangaren ƙirƙira da tsara shirye-shirye a kafafen rediyo da intanet.
Sauran sun haɗa da Idriss Abdallah Bako, Edita a ƙasar Ghana, wanda shi zai kula da shirye-shiryen gidan rediyon a Yammacin Afrika. Shi kuwa Souley Mumouni Barma, shi ne Edita, a Jamhuriyar Nijar, wanda kuma zai kula da Yankin Sahel. Sai Maimunatou Sadou, Edita a Jamhuriyar Kamaru kuma za ta kula da Tsakiyar Afrika.
Yayin da take magana daga babban ofishinta da ke Washington, D.C. Manajar-Edita ta ARI, Binta Suleiman Yero ta bayyana cewa: “Tsarin wannan kwamitin shugabanci, wata babbar alama ce ta ci gaba a tafiyarmu. Mun haɗa ƙwararrun masu hangen nesa daga fannoni daban-daban na jarida, sadarwa, fasahar zamani da kuma hulɗar al’umma. Hazakarsu za ta taimaka wajen cin ma burin ARI na haɗa kan ‘yan Afrika da ke cikin nahiyar da waɗanda ke ƙasashen waje, domin su sami murya mai ƙarfi a faɗin duniya.”

Sababbin shugabannin, ana sa ran za su kula da tafiyar da gidan rediyon cikin tsari, haɓaka shirye-shirye da gudanarwa, yayin da tashar ke shirin ƙaddamar da manyan shirye-shiryenta a faɗin Afrika da ma duniya baki ɗaya a gobe Juma’a.
Daga ƙarshe, ta ƙara da cewa: “Da waɗannan ƙwararrun ma’aikata da muke da su, ARI ta shirya tsaf don kafa sabon tarihi a harkar watsa labarai a Afrika. Burinmu shi ne isar da sahihan labarai, waɗanda ke da jan hankali da tattaunawar haɗin kai, waɗanda za su dace da masu sauraronmu daga sassa daban-daban na duniya.”
__________












