• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Tuesday, May 12, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 9, 2025
in Babban Labari
0
Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko

Babban Editan ARI na farko, Hassan Maina Kaina

214
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Hassan Maina Kaina


                       _______________
Hukumomin sabon Gidan Rediyon Afrika (Radio International – ARI), wanda zai fara gabatar da shirye-shiryensa a gobe Juma’a, ya naɗa shahararren ɗan jarida, Hassan Maina Kaina a matsayin Babban Edita kuma Shugaban Hukumar Gudanarwa (Editor-In-Chief/CEO).

Related posts

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

May 9, 2026
Yan ta’addan Daji Kafirai Ne  – Sarkin Musulmi

Yan ta’addan Daji Kafirai Ne – Sarkin Musulmi

May 8, 2026

Haka kuma, Hukumar gudanarwar, a wata takardar manema labarai da ta saki, ta sanar da sunayen shugabannin da za su jagoranci tashar rediyon, wacce aka kafa domin ƙarfafa muryoyin ‘yan Afrika da kuma gina labaran gaskiya na nahiyar.

Bayan Hassan, wanda aka naɗa a muƙamin Babban Edita kuma Shugaban Hukumar Gudanarwa, an kuma naɗa Mohammed Abba Jami’in Tsara Shirye-shirye da Tabbatar da Gudanuwar Ayyuka (Planner/Fixer). A’isha Mu’azu, ita ce Mataimakiyar Edita, wacce za ta jagoranci ɓangaren ƙirƙira da tsara shirye-shirye a kafafen rediyo da intanet.

Sauran sun haɗa da Idriss Abdallah Bako, Edita a ƙasar Ghana, wanda shi zai kula da shirye-shiryen gidan rediyon a Yammacin Afrika. Shi kuwa Souley Mumouni Barma, shi ne Edita, a Jamhuriyar Nijar, wanda kuma zai kula da Yankin Sahel. Sai Maimunatou Sadou, Edita a Jamhuriyar Kamaru kuma za ta kula da Tsakiyar Afrika.

Yayin da take magana daga babban ofishinta da ke Washington, D.C. Manajar-Edita ta ARI, Binta Suleiman Yero ta bayyana cewa: “Tsarin wannan kwamitin shugabanci, wata babbar alama ce ta ci gaba a tafiyarmu. Mun haɗa ƙwararrun masu hangen nesa daga fannoni daban-daban na jarida, sadarwa, fasahar zamani da kuma hulɗar al’umma. Hazakarsu za ta taimaka wajen cin ma burin ARI na haɗa kan ‘yan Afrika da ke cikin nahiyar da waɗanda ke ƙasashen waje, domin su sami murya mai ƙarfi a faɗin duniya.”

Hassan Maina Kaina a bakin aiki

Sababbin shugabannin, ana sa ran za su kula da tafiyar da gidan rediyon cikin tsari, haɓaka shirye-shirye da gudanarwa, yayin da tashar ke shirin ƙaddamar da manyan shirye-shiryenta a faɗin Afrika da ma duniya baki ɗaya a gobe Juma’a.

Daga ƙarshe, ta ƙara da cewa: “Da waɗannan ƙwararrun ma’aikata da muke da su, ARI ta shirya tsaf don kafa sabon tarihi a harkar watsa labarai a Afrika. Burinmu shi ne isar da sahihan labarai, waɗanda ke da jan hankali da tattaunawar haɗin kai, waɗanda za su dace da masu sauraronmu daga sassa daban-daban na duniya.”
__________

Previous Post

Prince Abdussamad Badamasi: Allah Tashi Kafaɗarka

Next Post

Abubakar Dalhatu Zurmi: A True Picture of a Patriot

Related Posts

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi
Babban Labari

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

May 9, 2026
Yan ta’addan Daji Kafirai Ne  – Sarkin Musulmi
Babban Labari

Yan ta’addan Daji Kafirai Ne – Sarkin Musulmi

May 8, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Next Post
Abubakar Dalhatu Zurmi: A True Picture of a Patriot

Abubakar Dalhatu Zurmi: A True Picture of a Patriot

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Bakan Gizo

August 27, 2023
TSOKACINMU NA YAU (13)

TSOKACINMU NA YAU (13)

March 13, 2025
EFCC Ta Kai Farmaki Jihar Katsina

Gamayyar Ƙungiyoyin Tsofaffin Ɗalibai Sun Roƙi Gwamnan Katsina Ya Girke Jami’ar Kimiyyar Lafiya A Malumfashi

June 27, 2023
Dokta Ɗanjuma Ya Tallafa Wa Mabuƙata Da Naira Miliyan 22

Dokta Ɗanjuma Ya Tallafa Wa Mabuƙata Da Naira Miliyan 22

June 30, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (12)
  • Malumfashi An Yi Babban Rashi
  • Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (12)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (12)

May 12, 2026
Malumfashi An Yi Babban Rashi

Malumfashi An Yi Babban Rashi

May 11, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.