• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, August 8, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
January 4, 2026
in Babban Labari
0
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

Zannan Galadiman Katsina, Dr. Tukur Hassan Tingilin

27
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami

Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami

July 31, 2026
Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama

Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama

July 30, 2026
Zannan Galadiman Katsina, Dr. Tukur Hassan Tingilin


                        __________
Manajan Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina kuma Shugaban Gidauniyar Zanna-Wali, Injiniya Tukur Hassan Tingilin ya bayyana cewa kishin ilimi da buƙatar ganin ilimi ya bunƙasa a yankunan Malumfashi da Ƙafur, shi ya sanya ya ɗauki nauyin bayar da tallafin karatu ga ɗaliban yankunan, su 110 da suka samu gurbin karatu a sabuwar babbar makarantar College of Agriculture and Technology ta Nabanje, Ƙaramar Hukumar Ƙafur, Jihar Katsina.

Dokta Tingilin, wanda shi ne Zannan Galadiman Katsina, Cigarin Danejin Katsina kuma Walin Ƙafur, ya bayyana cewa, kasancewar wannan makaranta ita ce ta farko mai girma a wannan yanki, ya zama wajibi ya nuna goyon baya ga mai girma Mai bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Siyasa, Alhaji Ibrahim Masari bisa ƙoƙarinsa na kawo ci cigaba a wannan yanki ta fuskar ilimi.

“Na daɗe ina kwaɗayin ganin yankinmu ya samu babbar makaranta, domin ilmantar da ɗinbin matasanmu maza da mata. Sai ga shi a ƙarƙashin mulkin Jam’iyyarmu ta APC, Allah ya ba mu shugabannin da ke kishinmu, suka kawo mana wannan makaranta. Don haka wajibi ne mu haɗa hannu domin taimaka wa al’ummarmu,” inji Injiniya Tingilin.

Ya ƙara da cewa: “Muna godiya ga mai girma Shugaban Ƙasa, Alhaji Bola Ahmed Tinubu da Mai ba shi shawara ta fuskar Siyasa, Alhaji Ibrahim Kabir Masari da kuma Mai girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa bisa ƙoƙarinsu na yi wa al’ummamu hidima a kowane lokaci.”

Da yake ƙarin bayani game da yadda wannan tallafin karatu zai kasance, Sakataren Giidauniyar Zanna-Wali, Malam Hassan Mukhtar Malumfashi ya ce, a kowacce Mazaɓar Kansila da ke ƙananan hukumomin Malumfashi da Ƙafur, su 22 za a zaɓi ɗalibai biyar-biyar. Wannan zai samar da jimillar ɗalibai 110 ke nan, waɗanda za su ci gajiyar wannan tallafi.

“Kuma dole sai ɗalibi yana da sakamakon jarabawar JAMB ta 2025 mai kyau, wadda za ta ba shi damar samun wannan tallafi na karatu, ƙarƙashin wannan gidauniya mai albarka,” a cewar Sakatare Hassan.

Ya ƙarƙare da cewa: “Kuma wannan karatu na National Diploma ne (ND), tsawon shekara biyu. Domin samun form na wannan tallafi ana iya tuntuɓar wakilan wannan gidauniya a yankin Malumfashi da Kafur, domin ƙarin bayani”
_______________

Previous Post

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (5)

Next Post

Hausa/Fulani: Together Forever

Related Posts

Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami
Babban Labari

Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami

July 31, 2026
Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama
Babban Labari

Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama

July 30, 2026
Yan Bindiga Sun Halaka Babban Jami’in Soja A Abuja
Babban Labari

Yan Bindiga Sun Halaka Babban Jami’in Soja A Abuja

July 28, 2026
Next Post
Hausa/Fulani: Together Forever

Hausa/Fulani: Together Forever

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

THE NIGERIAN ARMY AT 161 YEARS: Celebrating a Legacy of Bravery, Service and National Development

THE NIGERIAN ARMY AT 161 YEARS: Celebrating a Legacy of Bravery, Service and National Development

July 4, 2024
An Kammala Jana’izar Shugaba Buhari Cikin Jimami Da Alhini

An Kammala Jana’izar Shugaba Buhari Cikin Jimami Da Alhini

July 16, 2025
Ruhin Bukar Usman

Ruhin Bukar Usman

May 11, 2024
Daura Birnin Bayajidda: Janar Buratai Da Ayarinsa Sun Ziyarci Buhari Da Sarki

Daura Birnin Bayajidda: Janar Buratai Da Ayarinsa Sun Ziyarci Buhari Da Sarki

June 4, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Hukuma Ta Kafa Sabbin Sassa Domin Bunƙasa Al’umma A Jihar Katsina
  • Garin Zango Ya Samu Babban Asibiti na Farko A Tarihi
  • Zango Local Government Enjoys First-Ever General Hospital

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Hukuma Ta Kafa Sabbin Sassa Domin Bunƙasa Al’umma A Jihar Katsina

Hukuma Ta Kafa Sabbin Sassa Domin Bunƙasa Al’umma A Jihar Katsina

August 8, 2026
Garin Zango Ya Samu Babban Asibiti na Farko A Tarihi

Garin Zango Ya Samu Babban Asibiti na Farko A Tarihi

August 7, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.