Daga Rabi’u Na’auwa
Sanusi: Magajin Sanusi Da Kukuna
Wani tarihi mai kyau da matuƙar muhimmanci yana neman maimaita kansa a Jihar Kano.
Sarkin Kano na talatin da biyu a Daular Hausawa, Mohammadu Kukuna Ɗan Alhaji, bayan ya zama Sarkin Kano, ya yi mulki shekara guda. Madawakin Kano na lokacin ya ƙulla maƙarƙashiyar cire shi daga Sarkin Kano, suka naɗa Soyaki. Shi kuma Kukuna ya yi gudun hijira zuwa ƙasar Zariya.
Soyaki ya yi wata uku yana sarauta sai manyan Kano suka haɗu suka yi shawara
a kansa. Gaba ɗayan manyan masu ƙarfin ikon Kano a wancan lokacin suka haɗu a ƙarƙashin Galadima Wari, da Ɗan Iya Babba tare da Makama, suka yi shawarar dawo da Sarkin Kano Muhammadu Kukuna gadon sarautarsa.
Wannan ya sa suka ɗaura ɗamarar yaƙi da Sarkin Kano Soyaki, suka fitar da shi daga Kano. Muhmmadu Kukuna ya dawo karagar mulkinsa, shi kuma Soyaki aka gina masag ida a Dukarawa, inda ya rasu a can.
Wani abin al’ajabi da mamaki shi ne, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na biyu ya ɗauko tarihin Kakansa Muhammadu Sanusi na ɗaya tare da gadon duk wani
mataki da ya bi a loton sarautarsa a Daular Fulani, ta fuskar sauke dukkan nauyin da ya rataya a kan Sarki da talakawansa, a ilimance da zamanance da sauran matakai na rayuwa.
Wani tarihi da zai ƙara maimaita kansa shi ne, a jerin Sarakunan Hausawa ma,
Muhammadu Sanusi II ya ɗauko hanyar gadon Muhammadu Kukuna ɗan Alhaji,
kamar yadda aka cire Kukuna ta hanyar maƙarƙashiya, shi ma haka ta faru a kan
Muhammadu Sanusi II. Aka cire shi daga sarautarsa kamar yadda aka yi wa Kukuna.
Haka kuma kamar yadda Kukuna ya samu mafaka a Zariya kafin ya dawo karagar mulkinsa, haka shi ma Sanusi a ƙasar Zariya yake ƙarɓar gaisuwar mutanensa da ya yi wa nisa, sannan kuma a ƙasar Zariya yake gabatar da Sallar Idi.
Babban abin da zai ba ka mamaki shi ne, kamar yadda masu faɗa a ji a Jihar Kano suka ga cancantar dawowar Kukuna sarauta, haka yake a kan Muhammadu Sanusi. Shi ma mafi yawan masu faɗa a ji a Jihar Kano suna son su ga ranar da Sanusi zai dawo gadon sarautarsa. Haƙiƙa wannan ba ƙaramin abin al’ajabi ba ne.
A sarauta, dukkan wanda ya zamto Sarki, ana duba ga Sarakunan da suka gabata a
ga wa za a iya kwatanta shi da shi, ko ta fannin jarumta ko adalci ko jin ƙan talakawa da makamantansu. To amma ga Muhammadu Sanus,i shi al’amarinsa sai ya wuce dukkan yadda ake zato. Ga shi a zahiri ya yi gado ga Daular Fulani, gado irin na kwatance. Ya gama da wannan ɓangaren ya kuma tsallaka ga Daular Hausawa, ita ma ga shi zai ajiye muhimmin tarihin da ba a taɓa yin irinsa a tarihin ƙasar Hausa ba.
Haƙiƙa a idan haka ta tabbata, to Sanusi ya zama abin kwatance ko da kuwa a Daular Larabawa, domin samun gwarzon Sarki mai tagwayen tarihi yana da matuƙar wahala.
~~~~~~~
Na’auwa Marubuci ne kuma Mawallafi. Ya aiko da wannan sharhi daga Katsina.
~~~~~~~













