Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Manajan Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina kuma Shugaban Gidauniyar Zanna-Wali, Injiniya Tukur Hassan Tingilin ya bayyana cewa kishin ilimi da buƙatar ganin ilimi ya bunƙasa a yankunan Malumfashi da Ƙafur, shi ya sanya ya ɗauki nauyin bayar da tallafin karatu ga ɗaliban yankunan, su 110 da suka samu gurbin karatu a sabuwar babbar makarantar College of Agriculture and Technology ta Nabanje, Ƙaramar Hukumar Ƙafur, Jihar Katsina.
Dokta Tingilin, wanda shi ne Zannan Galadiman Katsina, Cigarin Danejin Katsina kuma Walin Ƙafur, ya bayyana cewa, kasancewar wannan makaranta ita ce ta farko mai girma a wannan yanki, ya zama wajibi ya nuna goyon baya ga mai girma Mai bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Siyasa, Alhaji Ibrahim Masari bisa ƙoƙarinsa na kawo ci cigaba a wannan yanki ta fuskar ilimi.
“Na daɗe ina kwaɗayin ganin yankinmu ya samu babbar makaranta, domin ilmantar da ɗinbin matasanmu maza da mata. Sai ga shi a ƙarƙashin mulkin Jam’iyyarmu ta APC, Allah ya ba mu shugabannin da ke kishinmu, suka kawo mana wannan makaranta. Don haka wajibi ne mu haɗa hannu domin taimaka wa al’ummarmu,” inji Injiniya Tingilin.
Ya ƙara da cewa: “Muna godiya ga mai girma Shugaban Ƙasa, Alhaji Bola Ahmed Tinubu da Mai ba shi shawara ta fuskar Siyasa, Alhaji Ibrahim Kabir Masari da kuma Mai girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa bisa ƙoƙarinsu na yi wa al’ummamu hidima a kowane lokaci.”
Da yake ƙarin bayani game da yadda wannan tallafin karatu zai kasance, Sakataren Giidauniyar Zanna-Wali, Malam Hassan Mukhtar Malumfashi ya ce, a kowacce Mazaɓar Kansila da ke ƙananan hukumomin Malumfashi da Ƙafur, su 22 za a zaɓi ɗalibai biyar-biyar. Wannan zai samar da jimillar ɗalibai 110 ke nan, waɗanda za su ci gajiyar wannan tallafi.
“Kuma dole sai ɗalibi yana da sakamakon jarabawar JAMB ta 2025 mai kyau, wadda za ta ba shi damar samun wannan tallafi na karatu, ƙarƙashin wannan gidauniya mai albarka,” a cewar Sakatare Hassan.
Ya ƙarƙare da cewa: “Kuma wannan karatu na National Diploma ne (ND), tsawon shekara biyu. Domin samun form na wannan tallafi ana iya tuntuɓar wakilan wannan gidauniya a yankin Malumfashi da Kafur, domin ƙarin bayani”
_______________













