Ministan Tsaro Janar Christopher Musa: Shawara Da Fatan Alheri
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Ta tabbata dai Janar Christopher Gwabi Musa shi ne sabon Ministan Tsaron Najeriya. Wannan kuwa ya biyo bayan wata wasiƙa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio. Shugaban ya miƙa sunan Janar Musa domin ya gaji Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, wanda ya yi murabus a ranar Litinin da ta gabata.
Janar Musa, mai shekaru 58, soja ne ƙwararre wanda ya yi aiki a matsayin Babban Hafsan Tsaro daga 2023 zuwa Oktoba 2025. Ya taɓa lashe Kambin Colin Powell a shekarar 2012 saboda ƙwarewarsa a aikin na soja.
An haifi Janar Musa a Sokoto a 1967, kuma ya yi makarantar firamare da sakandare a can kafin ya halarci College of Advanced Studies da ke Zariya. Ya kammala karatu a 1986 sannan ya shiga Nigerian Defence Academy a shekarar nan take, inda ya samu Digirin Farko a fannin Kimiyya, a shekarar 1991.
An ɗaura wa Janar Musa muƙamin Sakan Laftanar a 1991 kuma tun daga lokacin ya ci gaba da kyakkyawar tafiya a harkar soja. Daga cikin ofisoshin da ya taɓa riƙewa a gidan soja, suna haɗa da: General Staff Officer 1, Training/Operations a Hedikwatar Runduna ta 81 da Commanding Officer, Battalion ta 73 da Assistant Director, Operational Requirements, Department of Army Policy and Plans da Infantry Representative/Member, Training Team, HQ Nigerian Army Armour Corps.
A 2019, ya yi aiki a matsayin Deputy Chief of Staff, Training/Operations, Hedikwatar Infantry Centre and Corps. Ya taɓa zama Kwamandan, Sector 3, Operation Lafiya Dole da Kwamandan Sector 3, Multinational Joint Task Force a yankin Tafkin Chadi.
A 2021, an naɗa Janar Musa a matsayin Kwamandan Yaƙi na Operation Haɗin Kai. Daga baya kuma ya riƙe mukamin Kwamandan Rundunar Sojan Ƙasa, kafin daga bisani Shugaba Tinubu ya naɗa shi muƙamin Babban Hafsan Tsaro a 2023. Ya yi ritaya daga aikin soja a cikin watan Nuwamba da ya gabata.
Babu shakka Janar Musa ya samu shaidar nagarta daga sassa daban-daban na ƙasar nan. An shaide shi da cewa nagartaccen mutum ne da ba ruwansa da ƙabilanci. Haka kuma a lokacin da aka sanar da naɗa shi wannan muƙami na Ministan Tsaro, mutane da dama sun yi masa fatan alheri kuma sun ba da tabbacin cewa lallai an ajiye ƙwarya a daidai gurbinta.
A yayin da muke yi masa fatan alheri, bari kuma in ba shi wasu ‘yan shawarwari, domin ya fuskanci wannan sabon muƙami da gasken gaske. Wannan kuwa saboda la’akari da yanayin da ake ciki dangane da taɓarɓarewar harkokin tsaro a ƙasar nan fiye da tunanin mai tunani.
Ya Janar, ka fi ni sanin babban ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasar nan. A Arewa, ta’addancin ‘yan Boko Haram da takwarorinsu ba ɓoyayye ba ne a gare ka. Haka kuma kana sane da balahirar ‘yan bindiga, masu satar mutane domin kuɗin fansa. Haka ma a Kudancin Najeriya, kana sane da masu tada ƙayar baya domin kafa ƙasar Biyafara da sauransu. Lallai ne sai ka yi jan ido, ka haɗa kan jami’an tsaro, domin ganin an samu nasarar daƙile su.
Lallai ne ka yi duk mai yiwuwa, ka haɗa kai da masana tsaro da dukkan masu ruwa da tsaki a harkar tsaro domin shawara da kuma ɗaukar matakan da suka dace, domin samun nasara.
Muna yi maka fatan alheri tare da addu’ar Allah ya ba ka nasarar yin duk abin da ya dace, domin samar da zaman lafiya da ingantaccen tsaro a Najeriya.
_______________













