Kowa ya daɗe da sanin cewa a yau a Najeriya kuwane al’amari na rayuwa ya rataya ga makamashin man fetur.
Harkar sufuri, noma da kiwo, kasuwanci, aikin gwamnati, kamfanoni da ma harkar hutu da nishaɗi, duk sai da fetur suke murzawa. Da zarar farashinsa ya hau, daɗa farashin komai zai daɗu ba tare da jinkiri ba.
Muhimmancin da ke tattare da wannan haja ta fetur ta ƙara bayyana ƙarara tun daga shekaranjiya, biyo bayan jawabin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmad Tinubu, inda ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi adabo da batun TALLAFIN MAN FETUR.
Babu shakka wannan mataki na cire tallafi abin a yaba ne, musamman yadda rahotanni suka tabbatar da cewa dama TALLAFIN duk buge ce da harƙallar cuwa-cuwa, inda wasu ƙalilan ke amfana da shi, yayin da yawancin al’umma ke cutuwa.
Sai dai wani hanzari ba gudu ba, ya kamata Gwamnati ta tashi tsaye, ta yi jan ido, ta sa ƙafar wando ɗaya da ‘yan MAFIYAR MAI, domin daidaita al’amura. Lallai ne a yi duk mai yiwuwa wajen samar da farashin mai mai dacewa, yadda talaka zai samu sauƙin rayuwa.
Lallai ne a taka wa ‘yan kasuwar mai burki, domin su daina gallaza wa talaka. Lallai ne a samar da ingantattun matakan da za su samar da farashi mai kyau, yadda komai zai daidaita, ba cuta-ba-cutarwa!













