Shawara Ga Gwamnonin Arewa
Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
A jiya ne Ƙungiyar Gwamnonin Arewa sta kammala muhimmin taronta a Kaduna, inda suka cin ma matsaya kan al’amura da dama, dangane da magance matsalolin tsaro da sauransu, a Arewa.
Kaɗan daga cikin irin waɗannan matakai da suka ɗauka, sun haɗa da buƙatar Gwamnatin Tarayya ta soke lasisin masu haƙar ma’adinai a jihohin Arewa da goyon baya ga kafa ‘yan sandan jihohi da kuma batun asusun da zai riƙa tattara Naira biliyan ɗaya daga kowace jiha, a kowane wata, domin magance matsalolin tsaro.
Babu shakka gwamnonin sun yi tunani kan lamarin nan, sai dai kuma ina ganin ya kamata in ba su wasu ‘yan shawarwari, domin ƙarfafa gwiwa.
Ya kamata su maida hankali wajen amfani da waɗannan kuɗaɗe da za su tara, wajen farfaɗo da kamfanoni da masana’antu a Arewa, domin samar da ayyukan yi ga dubban matasan da ke zaman banza. Su maida hankali wajen bunƙasa harkokin noma da kiwo, wanda haka zai ƙara tallafa wa tattalin arziƙin al’umma. Hakan zai daƙile zaman banza da matasa suke yi, wanda shi ke ta’azzara aikata muggan laifuka da ta’addanci.
Haka kuma, ina ba da shawara, lallai ne gwamnonin Arewa su fuskanci bunƙasa ILIMI a Arewa, domin kuwa a halin yanzu ya taɓarɓare sosai kuma sauran duniya ta yi mana nisa sosai a wannan fanni.
Allah ya ba da ikon yin aiki da gaskiya da kishi, domin magance matsalolin tsaro da sauran matsalolin rayuwa da ke addabar al’umma. Amin-Summa-Amin!
_______________













