• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, May 2, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Lallai Ne A Sallami Shugaban Hukumar Zaɓe – Majalisar Musulunci

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
November 13, 2025
in Babban Labari
0
Lallai Ne A Sallami Shugaban Hukumar Zaɓe – Majalisar Musulunci

An buƙaci a sallami Shugaban INEC

26
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Lallai Ne A Sallami Shugaban Hukumar Zaɓe – Majalisar Musulunci

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026
An buƙaci a sallami Shugaban INEC


                             •••••••
Majalisar Ƙoli ta Addinin Musulunci ta Najeriya, wacce take ƙarƙashin jagorancin Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III ta fitar da wata sanarwa mai zafi, inda ta yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta korar sabon Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, bisa kalaman da ya furta, waɗanta majalisar ta ayyana a matsayin ƙazafi da cin mutunci ga addinin Musulunci.

Majalisar, a wata takardar manema labarai, ta bayyana cewa Farfesa Amupitan ya yi rubutu a kafar Soshalmidiya, inda ya danganta Shehu Usman Danfodiyo, wanda ake yi wa laƙabi da Mujaddadin Musulunci da yaɗuwar ta’addanci da kisan Kiristoci a Najeriya.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu

Wannan, a cewar Majalisar, babban sharri ne da kuma ƙoƙarin tozarta tarihi da martabar shahararren gwarzon Musulunci, wanda ya shimfiɗa ilimi da adalci a Arewacin Najeriya.

Bayan cikakken nazari da binciken kalaman Farfesan, Majalisar ta ce bai dace mutum mai irin wannan tunani ya ci gaba da riƙe muƙamin Shugaban Hukumar da ke da alhakin tafiyar da manyan zaɓe a ƙasar da take da mabiya addinai daban-daban ba. “Irin wannan ra’ayi, yana nuna wariya da tsana ga Musulunci da Musulmi kuma yana iya jefa ƙasar nan cikin rikici da rashin amincewa da tsarin zaɓe” a cewar sanarwar.

Haka kuma Majalisar ta yi Allah wadai da kalaman da ta kira “maganganun maƙiya Musulunci.” Ta kuma jaddada cewa Shehu Usman Danfodiyo ba ya da alaƙa da wani nau’i na ta’addanci ko tashin hankali. A maimakon haka, ya yi jihadi ne ta hanyar ilimi, adalci da wayar da kai waɗanda suka haifar da ci gaban al’umma a zamaninsa.

Majalisar ta kuma yi gargaɗin cewa, ba za ta lamunci cin zarafin Musulunci ko mashahuran shugabanninsa ba, musamman daga mutanen da suke riƙe da muƙaman gwamnati. Ta ce wannan lamari ya zama tamkar fitina da nuni da son zuciya, wanda zai iya lalata amincewar jama’a ga hukumomin gwamnati.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III

Majalisar ta Musulunci kuma ta yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da ya gaggauta ɗaukar mataki, domin kare mutuncin Musulmai da kuma tabbatar da cewa adalci ya tabbata a tsarin gwamnati. A cewar Majalisar, irin wannan lamari yana buƙatar tsauraran matakai don kauce wa tashin hankali da rikice-rikice masu tushe a addini.

Shugaban Hukumar Zaɓe, Farfesa Joash Amupitan

Majalisar ta roƙi Allah Maɗaukakin Sarki ya kare Musulunci daga sharrin maƙiya, ya tabbatar da zaman lafiya da adalci a Najeriya, tare da ɗaukaka kalmar Musulunci a cikin zuciyar dukkan bayinsa.
_______________

Previous Post

Ya Zama Wajibi A Ɗauki Mataki A Kan Minista Wike

Next Post

Muhammadu (Saw): Manzon Tsira Sha Yabo

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume
Babban Labari

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel
Babban Labari

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

April 2, 2026
Next Post
Muhammadu (Saw): Manzon Tsira Sha Yabo

Muhammadu (Saw): Manzon Tsira Sha Yabo

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Hararar Baba Ganduje

Hararar Baba Ganduje

June 29, 2023
TSOKACINMU NA YAU (19)

TSOKACINMU NA YAU (19)

March 19, 2025
Philip Chikwuedo Asiodu: A Legacy of Dedication and Service

Philip Chikwuedo Asiodu: A Legacy of Dedication and Service

December 16, 2025
Tinubu Ya Ba Nuhu Ribadu Muƙami

Tinubu Ya Ba Nuhu Ribadu Muƙami

June 15, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.