Ya Zama Wajibi A Ɗauki Mataki A Kan Minista Wike
Daga Janar Tukur Yusuf Buratai

•••••••
Abubuwan da suka faru a ranar 11 ga Nuwamba, 2025 tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya, Barista Nyesom Wike, sun yi munin da ya kamata a ɗauki mataki cikin gaugawa.
Kalaman da ya yi na tozarci ga wani jami’in sojan Najeriya mai sanye da khakin soja, ba kawai rashin ladabi ba ne, illa ce kai tsaye ga tsaron ƙasa da mutuncin gwamnati.
Harshen cin fuska da Minista ya yi wa jami’in soja, a yayin da yake kan aiki kuma cikin kayan aiki, halayya ce ta girman kai da rashin ɗa’a, wanda hakan ke barazana ga tsarin dokar ƙasa.
Wannan mataki ya keta tsarin umarni kai tsaye, ya nuna rashin girmama ikon Shugaban Ƙasa a matsayin Babban Kwamandan Askarawan Najeriya kuma wannan halayya ta Minista, ta raunata ƙarfin gwiwar dukkan jami’an tsaro da ke yi wa ƙasa hidima a ƙarƙashin tutar Najeriya. Irin wannan halayya tana lalata ginshiƙin ladabi da tsari da suka ta’allaƙa da tsarin gina tsaron ƙasa.
Ba za a iya kallon wannan lamari a matsayin lamarin siyasa ba. Wannan hatsari ne ga tsarin dokar ƙasa. Abin da Wike ya aikata yana nuna a fili cewa yana raina ikon Gwamnatin Tarayya.
Saboda haka, Barista Nyesom Wike dole ne ya nuna nadama a fili tare da neman afuwa daga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayinsa na Babban Kwamandan Askarawan Najeriya da kuma daga jami’in da ya tozarta.
Tsaron ƙasarmu ya fi komai muhimmanci. Lokaci ya yi da za a ɗauki mataki mai girma, kada a amince da siyasar cin fuskar sojoji. Mutuncin Rundunar Sojin Najeriya yana buƙatar tsarewa da darajawa.
√Togacciya: Janar Buratai ya wallafa wannan tsokaci ne da Ingilishi, a shafinsa na Facebook. Ni Bashir Yahuza Malumfashi na fassara shi zuwa Hausa.
_______________













