• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, July 26, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (13)

TSOKACI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
February 20, 2026
in Gizago
0
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (13)

Hausawa da Fulani abokan zumunta ne a Musulunci da zaman tare

23
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (13)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Saƙon Godiya Da Bangajiya

Saƙon Godiya Da Bangajiya

July 22, 2026
MALUMFASHI: Yau Haƙuri Ya Yi Rana

MALUMFASHI: Yau Haƙuri Ya Yi Rana

July 21, 2026

__________

Hausawa da Fulani abokan zumunta ne a Musulunci da zaman tare

√ Me Ya Sa Suke Kiran Masu Adawa Da Su Fulani?

Wani abin mamaki da rashin tunani na Hausawan Bogi, ‘Yan Ba-Zata shi ne, a kullum suka ga mutumin da ya saɓa da ra’ayinsu ko kuma yake tona asirin makircin da suke ƙulla wa al’umma, sai su ƙaƙaba masa rigar Fulani, su riƙa cewa shi Bafulatani ne, koda kuwa shi Bahaushe ne.

Haka kuma, tun daga lokacin za su ɗauki karan tsana su ɗora masa, koda kuwa ba su taɓa saninsa ko ganinsa ba a zahiri. Za ka ga suna tsine masa, suna ƙirƙirar labarun ƙarya suna jingina masa.

Waɗannan mutane suna yin haka ne da gangan kuma bisa manufar jefa ƙyama da tsanar ƙabilar Fulani. A gefe ɗaya kuma, domin su gwara kan Musulmi da haɗa husuma tsakanin al’ummar Arewa.

Su a rashin adalcinsu, duk wani mutum da ya fito daga ƙabilar Fulani, to ɗan ta’adda ne, komai gaskiyarsa, komai son zaman lafiyarsa, koda bai taɓa kashe ɗan tsako ba. Suna ɗora wa dukkan Fulani laifi ne saboda laifin da wasu ƙalilan na baragurbin Fulani ke aikatawa na ta’addanci. Amma kuma a gefe ɗaya, za ka ji suna yabon ‘yan ta’addan IPOB ko ‘yan ta’addan Birom da suke kashe Hausawa a Filato da sauran yankunan da suke kira Middlebelt.

Ni kuwa na ce, anya wannan adalci ne kuwa? Ta yaya za ka hukunta wata ƙabila gaba ɗayanta, bisa laifin da wasu tsirarun cikinta suke aikatawa?

Ko a jiya, wani mutum mai suna Salmanu Gwanzo, wanda nake kyautata zaton ɗan Ƙungiyar Hausawa Zalla ne, ya ƙalubalance ni, ya ce wai ina ba Fulani ‘yan ta’adda kariya; don haka Allanbaran ni Bafulatani ne. Shi ne na ba shi amsa kamar haka:

Ka ji tsoron Allah. Ka kawo mani rubutu ɗaya nawa, inda na taɓa kare FULANI ‘YAN TA’ADDA? Bal, ni ina cikin mutane sahun gaba da suke adawa da SULHUN DA AKE YI DA SU!

Idan ba ka taɓa gamuwa da rubutuna inda nake adawa da su ba, bari yau in jaddada matsayata a kan DUK WANI ƊAN TA’ADDA:

√ Ba na tare da duk wani mutum da ya ɗauki makami yana kashe al’umma, ko wane ne shi, ko wane ƙabila ne shi – BALARABE, BAHAUSHE, BAFULATANI, IBO, YORUBA, KATAF, ANGAS, BIROM, KANURI da sauransu.

√ Duk wanda ya aikata laifi (ƙarami ko babba) a hukunta sh,i shi kaɗai bisa laifin da ya aikata. AMMA KADA A SAKA DUKKAN ‘YAN ƘABILARSA, waɗanda ba su aikata laifin komai ba.

√ Laifin da ‘yan IPOB suka aikata, ba za a ɗora wa dukkan ƙabilar IBO ba.

√ Laifin da Area Boys suka aikata, ba za a ɗora wa dukkan YARABAWA ba.

√ Laifin da FULANIN DAJI suke aikatawa, ba za a ɗora wa dukkan ƙabilar FULANI ba.

√ Adalci shi ne, hukuma ta kama tare da hukunta duk wanda yake aikata laifi, shi kaɗai. Ba dukkan ‘yan ƙabilarsa ba, waɗanda ba su aikata laifin komai ba.

√ INA ROƘON ALLAH YA LA’ANCI DUK WASU ‘YAN TA’ADDA, KOWACE ƘABILA SUKE, KOWANE ADDINI SUKE, DA DUK MASU TAYA SU, DA DUK MASU JIN DAƊIN ABIN DA SUKE YI, DA DUK MASU ƊAURE MASU GINDI!

√ WANNAN ITA CE MATSAYATA HAR KULLUM!

__________

Previous Post

RAMADAN KARIM: 03-1447

Next Post

RAMADAN KARIM: 04-1447

Related Posts

Saƙon Godiya Da Bangajiya
Gizago

Saƙon Godiya Da Bangajiya

July 22, 2026
MALUMFASHI: Yau Haƙuri Ya Yi Rana
Gizago

MALUMFASHI: Yau Haƙuri Ya Yi Rana

July 21, 2026
Tsakanin Gwamna Bago Da Wasu Malamai…
Gizago

Tsakanin Gwamna Bago Da Wasu Malamai…

July 21, 2026
Next Post
RAMADAN KARIM: 04-1447

RAMADAN KARIM: 04-1447

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

SHERIF ALMUHAJIR: JAMA’A YA KAMATA MU MUTUNTA JUNA

SHERIF ALMUHAJIR: JAMA’A YA KAMATA MU MUTUNTA JUNA

August 3, 2024
BIU: A Visit to a City on a Plateau (3)

BIU: Ziyarar Babban Birni A Kan Tsauni (3)

December 23, 2023
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026
Na Wallafa Littattafai 89 A Shekara 25 – Sadiya Yakasai

Na Wallafa Littattafai 89 A Shekara 25 – Sadiya Yakasai

July 12, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • General Buratai to Marry Off His Daughter Today
  • Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya
  • Saƙon Godiya Da Bangajiya

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

July 25, 2026
Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

July 24, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.