Muhammadu (Saw): Manzon Tsira Sha Yabo
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
A yau Juma’a, rana wacce ita ce shugabar ranakun mako, rana ce da ake buƙatar mu yawaita salati da sallama ga fiyayyen talikai, Annabi Muhammadu, tsira da aminci su ƙara tabbata a gare shi da ahalinsa da sahabbansa da dukkan talikai da suka tsaya a tafarkinsa har zuwa ƙarshen duniya.
Yadda Juma’a take shugabar ranaku, Manzon Allah Muhammadu (saw) shi ne shugaban dukkan manzannin Allah. Shi ne ya fi kowa tarbiyya. Shi ne ya fi kowa tausayi da jin ƙai a cikin halittun Allah. Shi ne Allah ya aiko mana domin ya zama rahama ga dukkan halittunsa.
A yau Juma’a, mu nemi kusanci da Allah, ta hanyar yawaita salati ga Manzonsa, Muhammadu (saw). Mu yi tawassuli da ƙaunarsa, mu nemi dukkan abin da muke so daga Allah.
Ya Allah, kai ka ce mu roƙe ka. Kai ne mahaliccinmu, kai kaɗai muke wa bauta kuma kai kaɗai muke neman taimakonsa. Ba mu da ƙarfi, ba mu da iko sai kai kaɗai Allah. Kai ke da kowa kuma kai ke da komai.
Ya Allah, domin ƙaunar Manzonka, Bada dinka, Muhammadu (saw), Allah ka duba lamarinmu a ƙasar nan, ka kawo mana ƙarshen dukkan abin da muke tsoro. Ka ba mu aminci, aminci da aminci. Allah ka azurta mu da dukkan abin da yake arziki a gare ka, duniya da lahira. Ka kare mu daga dukkan sharri. Amin-Summa-Amin!
_______________













