TSOKACINMU NA YAU (14)
Yau Juma’a, 14-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 14-Maris-2025, Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
Ya ku ‘yan uwa, a jiya mun yi tsokaci ne game da gaskiya, yau kuma za mu duba kishiyarta; watau ƙarya.
Idan gaskiya tubali ce ta samar da nagartaccen ginin rayuwa, to ita ƙarya nakiya ce ta ruguza dukkan rayuwar mutum. Ƙarya, in ji masu hikima, linzamin Shaidan ce. Da ƙarya ce ake shuka duk wani mummunan aiki mai cutar da ɗan Adam.
Babban darasin tsoƙacinmu a nan shi ne, mu guji ɗabi’ar ƙarya. Mu yi ƙoƙarin korar ta daga dukkan al’amuran rayuwarmu, madamar dai muna son nasara da ci gaba a al’amuranmu na rayuwa.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













