Burna Boy: Fitaccen Mawaƙin Da Ya Rabauta Da Ni’imar Musulunci
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Fitaccen mawaƙin Afrobeats ɗan Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da Burna Boy, ya samu arzikin shiga inuwar Musulunci, inda a farkon makon nan ya bayyana cewa ya bar Kiristanci ya rungumi addinin Musulunci.
A cikin wata hira da aka yi da shi a kafar watsa labaran nishaɗi ta Plaqueboymax, mawaƙin wanda ya taɓa lashe kyautar Grammy ya ce ya taso a matsayin Kirista ne daga gidansu. Ya ce hakan ya faru ne saboda iyayensa Kirista ne, kamar yadda yankinsu ma ya kasance na mabiya addinin Kirista
Ko mene ne ya ja hankalinsa zuwa shiga Musulunci? Shahararren mawaƙi Burna Boy ya ce daga baya ne ya yanke shawarar rungumar Musulunci, bayan ya daɗe yana nazarin wasu addinai daban-daban domin neman cikakkiyar fahimta. Sai dai ya ce wannan bincike da nazari nasa sun haifar masa da ƙarin tambayoyi fiye da amsoshi, inda daga ƙarshe ya aminta da shiga Musulunci.
Ya ce: “Addini wani tsari ne na sarrafa rayuwa. A duk bincikena, kullum nakan gano cewa akwai wata hujjar kimiyya guda ɗaya, wacce ke saɓa wa kowane littafi. Komai yana fitowa ne daga wayewar rana.”
Ya ci gaba da cewa: “Ni mutum ne mai ruhi sosai. Na yi amanna da cewa mu halittu ne. Idan mu halittu ne, dole akwai mahaliccinmu. Na lura kowa da irin fassara da hangen da yake yi wa addini.
“Wannan shi ne abin da iyayenka suka yi imani da shi. Wannan shi ne abin da aka haife ka a ciki. Na tashi a matsayin Kirista amma daga baya na musulunta. Na barranta da duk sauran addinai, domin na yi nazari a kansu duka. Har yanzu ina ƙoƙarin gano wane addini ne na gaskiya kuma na ainihi?”
Mawaƙi Burna Boy, wanda ya canja suna zuwa Abdulkarim ya ci gaba da bayanin cewa: “Mafi yawan lokacin da nake binciken gaskiya, nakan fuskanci yawan ruɗani. Wannan ita ce matsalar. Abin da kawai na sani shi ne, gaskiya akwai wani abu a sama da ke kiyaye ni. Ina da alaƙa da wannan. Shi ya sa idan na yi addu’a, ina jin kamar ana sauraro na kuma ana amsa mani.”
√ Wane Ne Burna Boy?
An haifi Damini Ebunoluwa Ogulu, Burna Boy a ranar 2 ga Yuli 1991 a garin Fatakwal na Jihar Rivers, Najeriya. Ana yi masa laƙabi da African Giant, ODG da Big. Baya ga kasancewarsa mawaƙi, yana kuma sana’ar rubutawa da shirya waƙoƙi. Ya fara waɗannan sana’o’i tun daga shekarar 2010. Yana da kamfanin shirya waƙoƙi na Spaceship Records. Sunan mahaifinsa Samuel Ogulu, wanda yake da kamfanin yin walda. Mahaifiyarsa kuwa sunanta Bose Ogulu, wacce take aiki a matsayin tafinta. Yana da ‘yar uwa ɗaya, mai suna Nissi Ogulu.
Abdulkarim Burna Boy yana zaune ne a katafaren gidansa na alfarma da ke Unguwar Lekki, Legas, kodayake yana yawan zuwa Amurka domin sana’arsa ta waƙa, inda kuma yake da gida a birnin Los Angeles. Ya ƙware a salon waƙa iri huɗu, Afrobeats, Reggae, Dancehall da Pop.
Muna roƙon Allah ya dawwamar da shi cikin wannan addini na Musulunci kuma ya kasance mai ingantaccen imani har ƙarshen rayuwars. Amin-Summa-Amin.
‘Yan uwa, wane fatan alheri za ki yi wa ɗan uwa Abdulkarim Burna Boy? Ku bayyana a Comment Section.
_______________













