• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Nishadi

Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

NISHAƊI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 31, 2025
in Nishadi
0
Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

Sulhu alheri ne

4
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Rasuwar ‘Yar Kannywood Jidda Fulani: Ko Furodusa Aminu Saira Ya Kyauta?

Rasuwar ‘Yar Kannywood Jidda Fulani: Ko Furodusa Aminu Saira Ya Kyauta?

December 27, 2025
Burna Boy: Fitaccen Mawaƙin Da Ya Rabauta Da Ni’imar Musulunci

Burna Boy: Fitaccen Mawaƙin Da Ya Rabauta Da Ni’imar Musulunci

November 5, 2025
Sulhu alheri ne


                  _______________
A ‘yan kwanakin nan, kafafen sada zumunta sun cika da maganganu da rigima tsakanin A’isha Humaira, matar fitaccen mawaƙi Adamu Dauda Kahutu Rarara da ɗan wasan Hausa, Umar Baana. Wannan saɓani da ya samo asali daga maganganun da suka yi ta musaya, ya janyo hankalin jama’a, musamman masoyansu na masana’antar Kannywood.

A batu na gaskiya, ban ji daɗin wannan hatsaniya ba kuma lallai ya kamata Sarki Ali Nuhu da shi kansa Rarara su shigo cikin lamarin nan, domin a yi sulhu da kuma taka wa wannan fitina birki.

A matsayinmu na Musulmi kuma ‘yan Arewa, lallai ne mu zama masu taka-tsan-tsan da rayuwa. Allah (swt) a cikin littafinsa mai girma Alkur’ani, Suratul Hujurat, aya ta 9 yana cewa: “Idan ƙungiyoyi biyu daga cikin muminai suka yi faɗa, to ku sasanta tsakaninsu.” Wannan aya ta Alƙur’ani tana jaddada muhimmancin sulhu da zaman lafiya tsakanin ‘yan uwa Musulmi.

Ya ke babbar mata mai daraja, A’isha Humaira (sunan mahaifiyata ke na), ina son ki sani cewa a yanzu ke matar aure ce, kuma ana kallon ki da ƙima da daraja. Ana kallon ki a matsayin abin koyi ga mata da matasa. Ya kamata ki kiyaye duk wani furuci da halayen da za su iya zubar da mutuncinki da na mijinki. A matsayinki na mace mai aure, ya fi dacewa ki yi haƙuri da komai, ki bar maganar nan don Allah. Kada ki ce za ki zurfafa neman haƙƙinki zuwa kotu. Babu shakka ba a kyauta maki ba kuma Baana bai yi mutunci ba ko kaɗan, musamman da ya kama sunanki da na mijinki a soshalmidiya, yana ƙasƙantarwa. Amma duk da haka, don Allah ki share batun, domin kin riga kin yi sama, ke ba sa’arsa ba ce.

Kai kuma Umar Baana, kana iƙirarin cewa kai mai gyara ne, to ka sani, bai dace ba ko kaɗan ka ɗauko cin zarafi ka jefa ga matar aure, wai da sunan gyara ko nasiha kuma ka ɗora a soshalmidiya. Kai ma fa kana da iyali, ka haifa. Shin yaya za ka ji a ce wani ya ci zarafin matarka ko ɗiyarka, idan sun aikata wani kuskure a rayuwa? Don Allah ka kiyaye, ka san abin da ya kamata da wanda bai kamata ba. Neman suna ba hauka ba ne.

A wannan gaɓa, ina kira ga A’isha Humaira da Umar Baana, don Allah ku zauna ku yi tunani, ku sulhunta da juna. Ku yi haƙuri kuma ku gafarta wa juna. Domin kuwa babu abin da ke da daraja fiye da zaman lafiya, mutunci da sulhu; ba rigima da saɓani ba. Ku sani cewa shi sulhu alheri ne, kamar yadda Manzon Allah (saw) ya ce: “Shin ba zan gaya muku abin da ya fi daraja fiye da azumi da salla da sadaka ba? To shi ne sulhu tsakanin mutane, domin rigima tsakanin mutane tana ruguza addini.”

Wannan hadisi daga Abu Dawud, yana nuni da cewa zaman lafiya da fahimta sun fi rigima da tsokana daraja a gaban Allah. Allah sa mu dace, Amin.
______________

Previous Post

Aure Sunnar Manzo (saw): Isma’il Angon A’isha

Next Post

Taya Ni Mu Gyara: Kisan Baƙi Sai Gayya

Related Posts

Rasuwar ‘Yar Kannywood Jidda Fulani: Ko Furodusa Aminu Saira Ya Kyauta?
Nishadi

Rasuwar ‘Yar Kannywood Jidda Fulani: Ko Furodusa Aminu Saira Ya Kyauta?

December 27, 2025
Burna Boy: Fitaccen Mawaƙin Da Ya Rabauta Da Ni’imar Musulunci
Nishadi

Burna Boy: Fitaccen Mawaƙin Da Ya Rabauta Da Ni’imar Musulunci

November 5, 2025
KANNYWOOD JIYA DA YAU: DARASIN RAYUWA DAGA WASU TAURARI (1)
Nishadi

KANNYWOOD JIYA DA YAU: DARASIN RAYUWA DAGA WASU TAURARI (1)

August 3, 2025
Next Post
Taya Ni Mu Gyara: Kisan Baƙi Sai Gayya

Taya Ni Mu Gyara: Kisan Baƙi Sai Gayya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Abba Gida-Gida: Why Kano State is Too Big For His Shoes

Abba Gida-Gida: Why Kano State is Too Big For His Shoes

June 20, 2024
Ƙungiyar Marubutan Nahiyar Afirka (PAWA) Ta Buƙaci Marubuta Su Koma Yin Rubutu A Harsunan Gida

Ƙungiyar Marubutan Nahiyar Afirka (PAWA) Ta Buƙaci Marubuta Su Koma Yin Rubutu A Harsunan Gida

March 21, 2024
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

January 9, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (1)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (1)

December 26, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.