Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

_______________
A ‘yan kwanakin nan, kafafen sada zumunta sun cika da maganganu da rigima tsakanin A’isha Humaira, matar fitaccen mawaƙi Adamu Dauda Kahutu Rarara da ɗan wasan Hausa, Umar Baana. Wannan saɓani da ya samo asali daga maganganun da suka yi ta musaya, ya janyo hankalin jama’a, musamman masoyansu na masana’antar Kannywood.
A batu na gaskiya, ban ji daɗin wannan hatsaniya ba kuma lallai ya kamata Sarki Ali Nuhu da shi kansa Rarara su shigo cikin lamarin nan, domin a yi sulhu da kuma taka wa wannan fitina birki.
A matsayinmu na Musulmi kuma ‘yan Arewa, lallai ne mu zama masu taka-tsan-tsan da rayuwa. Allah (swt) a cikin littafinsa mai girma Alkur’ani, Suratul Hujurat, aya ta 9 yana cewa: “Idan ƙungiyoyi biyu daga cikin muminai suka yi faɗa, to ku sasanta tsakaninsu.” Wannan aya ta Alƙur’ani tana jaddada muhimmancin sulhu da zaman lafiya tsakanin ‘yan uwa Musulmi.
Ya ke babbar mata mai daraja, A’isha Humaira (sunan mahaifiyata ke na), ina son ki sani cewa a yanzu ke matar aure ce, kuma ana kallon ki da ƙima da daraja. Ana kallon ki a matsayin abin koyi ga mata da matasa. Ya kamata ki kiyaye duk wani furuci da halayen da za su iya zubar da mutuncinki da na mijinki. A matsayinki na mace mai aure, ya fi dacewa ki yi haƙuri da komai, ki bar maganar nan don Allah. Kada ki ce za ki zurfafa neman haƙƙinki zuwa kotu. Babu shakka ba a kyauta maki ba kuma Baana bai yi mutunci ba ko kaɗan, musamman da ya kama sunanki da na mijinki a soshalmidiya, yana ƙasƙantarwa. Amma duk da haka, don Allah ki share batun, domin kin riga kin yi sama, ke ba sa’arsa ba ce.
Kai kuma Umar Baana, kana iƙirarin cewa kai mai gyara ne, to ka sani, bai dace ba ko kaɗan ka ɗauko cin zarafi ka jefa ga matar aure, wai da sunan gyara ko nasiha kuma ka ɗora a soshalmidiya. Kai ma fa kana da iyali, ka haifa. Shin yaya za ka ji a ce wani ya ci zarafin matarka ko ɗiyarka, idan sun aikata wani kuskure a rayuwa? Don Allah ka kiyaye, ka san abin da ya kamata da wanda bai kamata ba. Neman suna ba hauka ba ne.
A wannan gaɓa, ina kira ga A’isha Humaira da Umar Baana, don Allah ku zauna ku yi tunani, ku sulhunta da juna. Ku yi haƙuri kuma ku gafarta wa juna. Domin kuwa babu abin da ke da daraja fiye da zaman lafiya, mutunci da sulhu; ba rigima da saɓani ba. Ku sani cewa shi sulhu alheri ne, kamar yadda Manzon Allah (saw) ya ce: “Shin ba zan gaya muku abin da ya fi daraja fiye da azumi da salla da sadaka ba? To shi ne sulhu tsakanin mutane, domin rigima tsakanin mutane tana ruguza addini.”
Wannan hadisi daga Abu Dawud, yana nuni da cewa zaman lafiya da fahimta sun fi rigima da tsokana daraja a gaban Allah. Allah sa mu dace, Amin.
______________













