GWAMNAN JIHAR NIGER YA ƘADDAMAR DA YAƘI DA TSAGERU DA ƁATAGARI
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Gwamnan Jihar Niger, Umar Muhammad Bago ya ƙaddamar da tsattsauran yaƙi da tsageru, ‘yan ta’adda da kuma ɓatagari.
Gwamnan ya ƙaddamar da sababbin dokoki ne a kan haka, waɗanda a cewarsa, za su taimaka wajen daƙile duk wata fitsara da barazanar tsaro a jihar. Haka kuma ya bayyana cewa dokokin zasu fara aiki nan take a faɗin jihar.
A cikin dokokin, Gwamnatin jihar ta Niger ta haramta bangar siyasa da duk wani abu mai kama da haka a faɗin jihar.
A tsarin dokokin, duk wanda aka same shi da wani makami da ya haɗa da wuƙa ko sanda, za a ɗauke shi a matsayin ɗan fashi da makami, idan kuma ya yi gardama da jami’an tsaro aka harbe shi da bindiga, to ba za a miƙa shi ga ‘yan uwansa ba, har sai sun biya kuɗin wannan alburushi da aka harbe shi da shi.
Duk wani namiji da aka samu da kitso ko dada a kansa, za a kama shi a kuma aske kan nasa.
An haramta amfani da babur da Keke-Napep daga ƙarfe shida na yamma zuwa shida na safe.
Wasu daga dokokin sun haɗa da cewa, duk wani mai Unguwa, Dagaci ko Hakimin da aka samu yana ɓoye ‘yan bangar siyasa, za a tsige shi kuma a kama shi. Duk wani gida da aka samu suna sayar da kowane irin nau’in kayan maye, za a rushe shi kuma a kama duk wanda aka samu a gidan.
Domin aiwatar da waɗannan sababbin dokoki, za a kafa kotu ta musamman ƙarƙashin kulawar babban Alƙalin jihar, wacce za ta kula da hukunta ‘yan bangar siyasa tare da tasa ƙeyarsu zuwa waƙafi. Jami’an tsaro za su sanya idanu sosai a wuraren da suka yi ƙaurin suna wajen aikata laifuka.
Haka kuma, duk wata mota da za ta shiga Babban Birnin Jihar Niger, wato Minna, idan aka same ta da duk wani nau’in kayan maye, za a ƙwace ta a sanya ta cikin asusun gwamnatin jihar.
Waɗannan tsauraran dokoki, ana sa ran za su magance matsaloli da barazanar tsaro a jihar.
______
Jama’a, mene ne ra’ayinku game da wannan babban mataki na Gwamnan Jihar Niger, Umar Muhammad Bago? Ku bayyana a Comment Section:
👇













